< Ayuba 13 >
1 “Idanuna sun ga waɗannan duka, kunnuwana sun ji sun kuma gane.
Eis que tudo isto viram os meus olhos, e os meus ouvidos o ouviram e entenderam.
2 Abin da kuka sani, ni ma na sani; ba ku fi ni ba.
Como vós o sabeis, o sei eu tambem; não vos sou inferior.
3 Amma ina so in yi magana da Maɗaukaki, in kai kukana wurin Allah kai tsaye.
Mas eu fallarei ao Todo-poderoso, e quero defender-me para com Deus.
4 Ku kuma kun ishe ni da ƙarairayi; ku likitocin wofi ne, dukanku!
Vós porém sois inventores de mentiras, e vós todos medicos que não valem nada.
5 In da za ku yi shiru gaba ɗaya! Zai zama muku hikima.
Oxalá vos calasseis de todo! que isso seria a vossa sabedoria.
6 Ku ji gardamata yanzu; ku ji roƙon da zai fito daga bakina.
Ouvi agora a minha defeza, e escutae os argumentos dos meus labios.
7 Za ku iya yin muguwar magana a madadin Allah? Ko za ku yi ƙarya a madadinsa?
Porventura por Deus fallareis perversidade? e por elle fallareis engano?
8 Ko za ku nuna masa sonkai? Ko za ku yi gardama a madadinsa?
Ou fareis acceitação da sua pessoa? ou contendereis por Deus?
9 In ya bincike ku zai tarar ba ku da laifi? Ko za ku iya ruɗe shi yadda za ku ruɗi mutane?
Ser-vos-hia bom, se elle vos esquadrinhasse? ou zombareis d'elle, como se zomba d'algum homem?
10 Ba shakka zai kwaɓe ku in kun nuna sonkai a ɓoye.
Certamente vos reprehenderá, se em occulto fizerdes acceitação de pessoas.
11 Ko ikonsa ba ya ba ku tsoro? Tsoronsa ba zai auka muku ba?
Porventura não vos espantará a sua alteza? e não cairá sobre vós o seu temor?
12 Duk surutanku kamar toka suke; kāriyarku na yimɓu ne.
As vossas memorias são como a cinza: as vossas alturas como alturas de lodo.
13 “Ku yi shiru zan yi magana; sa’an nan abin da zai same ni yă same ni.
Calae-vos perante mim, e fallarei eu, e que fique alliviado algum tanto.
14 Don me na sa kaina cikin hatsari na yi kasada da raina?
Por que razão tomo eu a minha carne com os meus dentes, e ponho a minha vida na minha mão?
15 Ko da zai kashe ni ne, begena a cikinsa zai kasance; ba shakka zan kāre kaina a gabansa
Ainda que me matasse, n'elle esperarei; comtudo os meus caminhos defenderei diante d'elle.
16 lalle wannan zai kawo mini kuɓuta gama ba wani marar tsoron Allah da zai iya zuwa wurinsa!
Tambem elle será a salvação minha: porém o hypocrita não virá perante o seu rosto
17 Ku saurara da kyau ku ji abin da zan faɗa; bari kunnuwanku su ji abin da zan ce.
Ouvi com attenção as minhas razões, e com os vossos ouvidos a minha declaração.
18 Yanzu da na shirya ƙarata, na san za a ce ba ni da laifi.
Eis que já tenho ordenado a minha causa, e sei que serei achado justo.
19 Ko wani zai ce ga laifin da na yi? In an same ni da laifi, zan yi shiru in mutu.
Quem é o que contenderá comigo? se eu agora me calasse, daria o espirito.
20 “Kai dai biya mini waɗannan bukatu biyu kawai ya Allah, ba zan kuwa ɓoye daga gare ka ba;
Duas coisas sómente não faças para comigo; então me não esconderei do teu rosto:
21 Ka janye hannunka nesa da ni, ka daina ba ni tsoro da bantsoronka.
Desvia a tua mão para longe, de sobre mim, e não me espante o teu terror.
22 Sa’an nan ka kira ni, zan kuwa amsa, ko kuma ka bar ni in yi magana sai ka amsa mini.
Chama, pois, e eu responderei; ou eu fallarei, e tu responde-me.
23 Abubuwa nawa na yi waɗanda ba daidai ba, kuma zunubi ne? Ka nuna mini laifina da zunubina.
Quantas culpas e peccados tenho eu? notifica-me a minha transgressão e o meu peccado.
24 Don me ka ɓoye mini fuskarka; ka kuma sa na zama kamar maƙiyinka?
Porque escondes o teu rosto, e me tens por teu inimigo?
25 Ko za a wahalar da ganye wanda iska take hurawa? Ko za ka bi busasshiyar ciyawa?
Porventura quebrantarás a folha arrebatada do vento? e perseguirás o restolho secco?
26 Gama ka rubuta abubuwa marasa daɗi game da ni; ka sa na yi gādon zunuban ƙuruciyata.
Porque escreves contra mim amarguras e me fazes herdar as culpas da minha mocidade?
27 Ka daure ƙafafuna da sarƙa; kana kallon duk inda na taka ta wurin sa shaida a tafin ƙafafuna.
Tambem pões no tronco os meus pés, e observas todos os meus caminhos, e marcas as solas dos meus pés.
28 “Haka mutum yake lalacewa kamar ruɓaɓɓen abu, kamar rigar da asu ya cinye.
Envelhecendo-se entretanto elle com a podridão, e como o vestido, ao qual roe a traça.