< Ayuba 13 >
1 “Idanuna sun ga waɗannan duka, kunnuwana sun ji sun kuma gane.
Redzi, to visu mana acs redzējusi, mana auss dzirdējusi un to likusi vērā.
2 Abin da kuka sani, ni ma na sani; ba ku fi ni ba.
Ko jūs protat, to es arīdzan protu, jūs man neesat priekšā.
3 Amma ina so in yi magana da Maɗaukaki, in kai kukana wurin Allah kai tsaye.
Bet es gribu runāt uz to Visuvareno, un man gribās aizbildināties tā stiprā Dieva priekšā.
4 Ku kuma kun ishe ni da ƙarairayi; ku likitocin wofi ne, dukanku!
Jo tiešām, jūs esat melu runātāji, jūs visi esat nelietīgi dziednieki.
5 In da za ku yi shiru gaba ɗaya! Zai zama muku hikima.
Kaut jūs pavisam klusu būtu, tas jums būtu par gudrību.
6 Ku ji gardamata yanzu; ku ji roƙon da zai fito daga bakina.
Klausiet jel manu aizbildināšanos, un ņemiet vērā manas mutes tiesāšanos.
7 Za ku iya yin muguwar magana a madadin Allah? Ko za ku yi ƙarya a madadinsa?
Vai gribat netaisnību runāt Dieva labad un Viņa labad izteikt viltību?
8 Ko za ku nuna masa sonkai? Ko za ku yi gardama a madadinsa?
Vai Viņu gribat aizbildināt un Dievam būt pārstāvētāji?
9 In ya bincike ku zai tarar ba ku da laifi? Ko za ku iya ruɗe shi yadda za ku ruɗi mutane?
Vai būs labi, kad Viņš jūs meklēs, vai Viņu pievilsiet, kā cilvēku pieviļ?
10 Ba shakka zai kwaɓe ku in kun nuna sonkai a ɓoye.
Sodīt Viņš jūs sodīs, ja jūs slepeni vaigu uzlūkojat.
11 Ko ikonsa ba ya ba ku tsoro? Tsoronsa ba zai auka muku ba?
Vai Viņa augstība jūs neiztrūcinās un bailes no Viņa jums neuzkritīs?
12 Duk surutanku kamar toka suke; kāriyarku na yimɓu ne.
Jūsu mācības būs kā pelni, un jūsu augstie vārdi kā mālu kopas.
13 “Ku yi shiru zan yi magana; sa’an nan abin da zai same ni yă same ni.
Palieciet man klusu, un es runāšu, lai man notiek, kas notikdams.
14 Don me na sa kaina cikin hatsari na yi kasada da raina?
Kāpēc man savu miesu bija zobos ņemt, un savu dvēseli likt savā rokā?
15 Ko da zai kashe ni ne, begena a cikinsa zai kasance; ba shakka zan kāre kaina a gabansa
Redzi, jebšu Viņš mani nokaus, taču es uz Viņu gribu cerēt, es tikai savus ceļus gribu aizbildināt Viņa priekšā.
16 lalle wannan zai kawo mini kuɓuta gama ba wani marar tsoron Allah da zai iya zuwa wurinsa!
Jau tas man būs par pestīšanu, ka viltnieks Viņa priekšā nenāks.
17 Ku saurara da kyau ku ji abin da zan faɗa; bari kunnuwanku su ji abin da zan ce.
Klausāties, klausāties manus vārdus, un mana valoda lai skan jūsu ausīs.
18 Yanzu da na shirya ƙarata, na san za a ce ba ni da laifi.
Redzat jel, es esmu gatavs uz tiesu, es zinu, ka man paliks taisnība.
19 Ko wani zai ce ga laifin da na yi? In an same ni da laifi, zan yi shiru in mutu.
Kas ar mani varētu tiesāties? Patiesi tad es ciestu klusu un mirtu.
20 “Kai dai biya mini waɗannan bukatu biyu kawai ya Allah, ba zan kuwa ɓoye daga gare ka ba;
Divas lietas tikai man nedari, tad es neapslēpšos Tavā priekšā.
21 Ka janye hannunka nesa da ni, ka daina ba ni tsoro da bantsoronka.
Lai Tava roka paliek tālu no manis, un Tava briesmība lai mani neizbiedē.
22 Sa’an nan ka kira ni, zan kuwa amsa, ko kuma ka bar ni in yi magana sai ka amsa mini.
Tad sauc, un es atbildēšu, vai es runāšu, un Tu atbildi man.
23 Abubuwa nawa na yi waɗanda ba daidai ba, kuma zunubi ne? Ka nuna mini laifina da zunubina.
Cik man ir noziegumu un grēku? Dari man zināmus manus grēkus un manus pārkāpumus.
24 Don me ka ɓoye mini fuskarka; ka kuma sa na zama kamar maƙiyinka?
Kāpēc Tu apslēpi Savu vaigu un mani turi par Savu ienaidnieku?
25 Ko za a wahalar da ganye wanda iska take hurawa? Ko za ka bi busasshiyar ciyawa?
Vai Tu biedināsi šaubīgu lapu un vajāsi izkaltušus rugājus.
26 Gama ka rubuta abubuwa marasa daɗi game da ni; ka sa na yi gādon zunuban ƙuruciyata.
Jo Tu man nospriedi rūgtumus un lieci manīt manas jaunības noziegumus.
27 Ka daure ƙafafuna da sarƙa; kana kallon duk inda na taka ta wurin sa shaida a tafin ƙafafuna.
Tu lieci manas kājas siekstā un glūni uz visiem maniem ceļiem un ieslēdzi manas pēdas aplokā, -
28 “Haka mutum yake lalacewa kamar ruɓaɓɓen abu, kamar rigar da asu ya cinye.
Un tomēr šis iznīkst kā trūdi, tā kā drēbe, ko kodes saēd.