< Ayuba 13 >

1 “Idanuna sun ga waɗannan duka, kunnuwana sun ji sun kuma gane.
視よわが目これを盡く觀 わが耳これを聞て通逹れり
2 Abin da kuka sani, ni ma na sani; ba ku fi ni ba.
汝らが知るところは我もこれを知る 我は汝らに劣らず
3 Amma ina so in yi magana da Maɗaukaki, in kai kukana wurin Allah kai tsaye.
然りと雖ども我は全能者に物言ん 我は神と論ぜんことをのぞむ
4 Ku kuma kun ishe ni da ƙarairayi; ku likitocin wofi ne, dukanku!
汝らは只謊言を造り設くる者 汝らは皆無用の醫師なり
5 In da za ku yi shiru gaba ɗaya! Zai zama muku hikima.
願くは汝ら全く默せよ 然するは汝らの智慧なるべし
6 Ku ji gardamata yanzu; ku ji roƙon da zai fito daga bakina.
請ふわが論ずる所を聽き 我が唇にて辨爭そふ所を善く聽け
7 Za ku iya yin muguwar magana a madadin Allah? Ko za ku yi ƙarya a madadinsa?
神のために汝ら惡き事を言や 又かれのために虚僞を述るや
8 Ko za ku nuna masa sonkai? Ko za ku yi gardama a madadinsa?
汝ら神の爲に偏るや またかれのために爭はんとするや
9 In ya bincike ku zai tarar ba ku da laifi? Ko za ku iya ruɗe shi yadda za ku ruɗi mutane?
神もし汝らを鑒察たまはば豈善らんや 汝等人を欺むくごとくに彼を欺むき得んや
10 Ba shakka zai kwaɓe ku in kun nuna sonkai a ɓoye.
汝等もし密に私しするあらば彼かならず汝らを責ん
11 Ko ikonsa ba ya ba ku tsoro? Tsoronsa ba zai auka muku ba?
その威光なんぢらを懼れしめざらんや 彼を懼るる畏懼なんぢらに臨まざらんや
12 Duk surutanku kamar toka suke; kāriyarku na yimɓu ne.
なんぢらの諭言は灰に譬ふべし なんぢらの城は土の城となる
13 “Ku yi shiru zan yi magana; sa’an nan abin da zai same ni yă same ni.
默して我にかかはらざれ 我言語んとす 何事にもあれ我に來らば來れ
14 Don me na sa kaina cikin hatsari na yi kasada da raina?
我なんぞ我肉をわが齒の間に置き わが生命をわが手に置かんや
15 Ko da zai kashe ni ne, begena a cikinsa zai kasance; ba shakka zan kāre kaina a gabansa
彼われを殺すとも我は彼に依頼まん 唯われは吾道を彼の前に明かにせんとす
16 lalle wannan zai kawo mini kuɓuta gama ba wani marar tsoron Allah da zai iya zuwa wurinsa!
彼また終に我救拯とならん 邪曲なる者は彼の前にいたること能はざればなり
17 Ku saurara da kyau ku ji abin da zan faɗa; bari kunnuwanku su ji abin da zan ce.
なんぢら聽よ 我言を聽け我が述る所をなんぢらの耳に入しめよ
18 Yanzu da na shirya ƙarata, na san za a ce ba ni da laifi.
視よ我すでに吾事を言竝べたり 必ず義しとせられんと自ら知る
19 Ko wani zai ce ga laifin da na yi? In an same ni da laifi, zan yi shiru in mutu.
誰か能くわれと辨論ふ者あらん 若あらば我は口を緘て死ん
20 “Kai dai biya mini waɗannan bukatu biyu kawai ya Allah, ba zan kuwa ɓoye daga gare ka ba;
惟われに二の事を爲たまはざれ 然ば我なんぢの面をさけて隱れじ
21 Ka janye hannunka nesa da ni, ka daina ba ni tsoro da bantsoronka.
なんぢの手を我より離したまへ 汝の威嚴をもて我を懼れしめたまはざれ
22 Sa’an nan ka kira ni, zan kuwa amsa, ko kuma ka bar ni in yi magana sai ka amsa mini.
而して汝われを召したまへ 我こたへん 又われにも言はしめて汝われに答へたまへ
23 Abubuwa nawa na yi waɗanda ba daidai ba, kuma zunubi ne? Ka nuna mini laifina da zunubina.
我の愆われの罪いくばくなるや 我の背反と罪とを我に知しめたまへ
24 Don me ka ɓoye mini fuskarka; ka kuma sa na zama kamar maƙiyinka?
何とて御顏を隱し我をもて汝の敵となしたまふや
25 Ko za a wahalar da ganye wanda iska take hurawa? Ko za ka bi busasshiyar ciyawa?
なんぢは吹廻さるる木の葉を威し 干あがりたる籾殼を追ひたまふや
26 Gama ka rubuta abubuwa marasa daɗi game da ni; ka sa na yi gādon zunuban ƙuruciyata.
汝は我につきて苦き事等を書しるし 我をして我が幼稚時の罪を身に負しめ
27 Ka daure ƙafafuna da sarƙa; kana kallon duk inda na taka ta wurin sa shaida a tafin ƙafafuna.
わが足を足械にはめ 我すべての道を伺ひ我足の周圍に限界をつけたまふ
28 “Haka mutum yake lalacewa kamar ruɓaɓɓen abu, kamar rigar da asu ya cinye.
我は腐れたる者のごとくに朽ゆき 蠹に食るる衣服に等し

< Ayuba 13 >