< Ayuba 13 >
1 “Idanuna sun ga waɗannan duka, kunnuwana sun ji sun kuma gane.
Siehe, das hat alles mein Auge gesehen und mein Ohr gehöret, und habe es verstanden.
2 Abin da kuka sani, ni ma na sani; ba ku fi ni ba.
Was ihr wisset, das weiß ich auch, und bin nicht geringer denn ihr.
3 Amma ina so in yi magana da Maɗaukaki, in kai kukana wurin Allah kai tsaye.
Doch wollte ich gerne wider den Allmächtigen reden und wollte gerne mit Gott rechten.
4 Ku kuma kun ishe ni da ƙarairayi; ku likitocin wofi ne, dukanku!
Denn ihr deutet es fälschlich und seid alle unnütze Ärzte.
5 In da za ku yi shiru gaba ɗaya! Zai zama muku hikima.
Wollte Gott, ihr schwieget; so würdet ihr weise.
6 Ku ji gardamata yanzu; ku ji roƙon da zai fito daga bakina.
Höret doch meine Strafe und merket auf die Sache, davon ich rede.
7 Za ku iya yin muguwar magana a madadin Allah? Ko za ku yi ƙarya a madadinsa?
Wollt ihr Gott verteidigen mit Unrecht und für ihn List brauchen?
8 Ko za ku nuna masa sonkai? Ko za ku yi gardama a madadinsa?
Wollt ihr seine Person ansehen? Wollt ihr Gott vertreten?
9 In ya bincike ku zai tarar ba ku da laifi? Ko za ku iya ruɗe shi yadda za ku ruɗi mutane?
Wird's euch auch wohlgehen, wenn er euch richten wird? Meinet ihr, daß ihr ihn täuschen werdet, wie man einen Menschen täuschet?
10 Ba shakka zai kwaɓe ku in kun nuna sonkai a ɓoye.
Er wird euch strafen, wo ihr Person ansehet heimlich.
11 Ko ikonsa ba ya ba ku tsoro? Tsoronsa ba zai auka muku ba?
Wird er euch nicht erschrecken, wenn er sich wird hervortun, und seine Furcht wird über euch fallen?
12 Duk surutanku kamar toka suke; kāriyarku na yimɓu ne.
Euer Gedächtnis wird verglichen werden der Asche, und euer Rücken wird wie ein Leimenhaufe sein.
13 “Ku yi shiru zan yi magana; sa’an nan abin da zai same ni yă same ni.
Schweiget mir, daß ich rede; es soll mir nichts fehlen.
14 Don me na sa kaina cikin hatsari na yi kasada da raina?
Was soll ich mein Fleisch mit meinen Zähnen beißen und meine Seele in meine Hände legen?
15 Ko da zai kashe ni ne, begena a cikinsa zai kasance; ba shakka zan kāre kaina a gabansa
Siehe, er wird mich doch erwürgen, und ich kann's nicht erwarten; doch will ich meine Wege vor ihm strafen.
16 lalle wannan zai kawo mini kuɓuta gama ba wani marar tsoron Allah da zai iya zuwa wurinsa!
Er wird ja mein Heil sein; denn es kommt kein Heuchler vor ihn.
17 Ku saurara da kyau ku ji abin da zan faɗa; bari kunnuwanku su ji abin da zan ce.
Höret meine Rede und meine Auslegung vor euren Ohren!
18 Yanzu da na shirya ƙarata, na san za a ce ba ni da laifi.
Siehe, ich habe das Urteil schon gefället; ich weiß, daß ich werde gerecht sein.
19 Ko wani zai ce ga laifin da na yi? In an same ni da laifi, zan yi shiru in mutu.
Wer ist, der mit mir rechten will? Aber nun muß ich schweigen und verderben.
20 “Kai dai biya mini waɗannan bukatu biyu kawai ya Allah, ba zan kuwa ɓoye daga gare ka ba;
Zweierlei tu mir nur nicht, so will ich mich vor dir nicht verbergen:
21 Ka janye hannunka nesa da ni, ka daina ba ni tsoro da bantsoronka.
Laß deine Hand ferne von mir sein, und dein Schrecken erschrecke mich nicht.
22 Sa’an nan ka kira ni, zan kuwa amsa, ko kuma ka bar ni in yi magana sai ka amsa mini.
Rufe mir, ich will dir antworten; oder ich will reden, antworte du mir.
23 Abubuwa nawa na yi waɗanda ba daidai ba, kuma zunubi ne? Ka nuna mini laifina da zunubina.
Wie viel ist meiner Missetat und Sünden? Laß mich wissen meine Übertretung und Sünde!
24 Don me ka ɓoye mini fuskarka; ka kuma sa na zama kamar maƙiyinka?
Warum verbirgest du dein Antlitz und hältst mich für deinen Feind?
25 Ko za a wahalar da ganye wanda iska take hurawa? Ko za ka bi busasshiyar ciyawa?
Willst du wider ein fliegend Blatt so ernst sein und einen dürren Halm verfolgen?
26 Gama ka rubuta abubuwa marasa daɗi game da ni; ka sa na yi gādon zunuban ƙuruciyata.
Denn du schreibest mir an Betrübnis und willst mich umbringen um der Sünden willen meiner Jugend.
27 Ka daure ƙafafuna da sarƙa; kana kallon duk inda na taka ta wurin sa shaida a tafin ƙafafuna.
Du hast meinen Fuß in Stock gelegt und hast acht auf alle meine Pfade und siehest auf die Fußtapfen meiner Füße,
28 “Haka mutum yake lalacewa kamar ruɓaɓɓen abu, kamar rigar da asu ya cinye.
der ich doch wie ein faul Aas vergehe und wie ein Kleid, das die Motten fressen.