< Ayuba 13 >

1 “Idanuna sun ga waɗannan duka, kunnuwana sun ji sun kuma gane.
Voilà que mon œil a vu toutes ces choses, et que mon oreille les a ouïes, et que je les ai comprises une à une.
2 Abin da kuka sani, ni ma na sani; ba ku fi ni ba.
Et je sais, moi aussi, selon votre science, et je ne suis point inférieur à vous.
3 Amma ina so in yi magana da Maɗaukaki, in kai kukana wurin Allah kai tsaye.
Mais cependant c’est au Tout-Puissant que je parlerai, et c’est avec Dieu que je désire m’entretenir,
4 Ku kuma kun ishe ni da ƙarairayi; ku likitocin wofi ne, dukanku!
En montrant auparavant que vous êtes des fabricateurs de mensonge et des défenseurs de maximes perverses.
5 In da za ku yi shiru gaba ɗaya! Zai zama muku hikima.
Et plût à Dieu que vous gardiez le silence! Vous pourriez passer pour sages.
6 Ku ji gardamata yanzu; ku ji roƙon da zai fito daga bakina.
Ecoutez donc ma réprimande, et soyez attentifs au jugement de mes lèvres.
7 Za ku iya yin muguwar magana a madadin Allah? Ko za ku yi ƙarya a madadinsa?
Est-ce que Dieu a besoin de votre mensonge, de manière que vous parliez pour lui un langage artificieux?
8 Ko za ku nuna masa sonkai? Ko za ku yi gardama a madadinsa?
Est-ce que vous faites acception de sa personne, et que vous vous efforcez de juger en faveur de Dieu?
9 In ya bincike ku zai tarar ba ku da laifi? Ko za ku iya ruɗe shi yadda za ku ruɗi mutane?
Ou cela lui plaira-t-il, lui à qui rien ne peut être caché? Ou bien sera-t-il trompé comme un homme par vos artifices?
10 Ba shakka zai kwaɓe ku in kun nuna sonkai a ɓoye.
Lui-même vous blâmera, parce qu’en secret vous faites acception de sa personne.
11 Ko ikonsa ba ya ba ku tsoro? Tsoronsa ba zai auka muku ba?
Aussitôt qu’il s’émouvra, il vous troublera, et sa terreur fondra sur vous.
12 Duk surutanku kamar toka suke; kāriyarku na yimɓu ne.
Votre mémoire sera semblable à la cendre, et vos têtes superbes seront réduites en boue.
13 “Ku yi shiru zan yi magana; sa’an nan abin da zai same ni yă same ni.
Gardez un peu de temps le silence, afin que je dise tout ce que mon esprit me suggérera.
14 Don me na sa kaina cikin hatsari na yi kasada da raina?
Pourquoi déchiré-je ma chair avec mes dents? Et pourquoi porté-je mon âme entre mes mains?
15 Ko da zai kashe ni ne, begena a cikinsa zai kasance; ba shakka zan kāre kaina a gabansa
Quand il me tuerait, c’est en lui que j’espérerais; j’exposerai donc mes voies en sa présence.
16 lalle wannan zai kawo mini kuɓuta gama ba wani marar tsoron Allah da zai iya zuwa wurinsa!
Et lui-même sera mon sauveur; car aucun hypocrite ne viendra en sa présence.
17 Ku saurara da kyau ku ji abin da zan faɗa; bari kunnuwanku su ji abin da zan ce.
Ecoutez mon discours, prêtez l’oreille à des énigmes.
18 Yanzu da na shirya ƙarata, na san za a ce ba ni da laifi.
Si j’étais jugé, je sais que je serais trouvé innocent.
19 Ko wani zai ce ga laifin da na yi? In an same ni da laifi, zan yi shiru in mutu.
Qui est celui qui veut entrer en jugement avec moi? Qu’il vienne: pourquoi me consumerais-je en me taisant?
20 “Kai dai biya mini waɗannan bukatu biyu kawai ya Allah, ba zan kuwa ɓoye daga gare ka ba;
Seulement, ô Dieu, ne me faites pas deux choses, et je ne me cacherai pas devant votre face:
21 Ka janye hannunka nesa da ni, ka daina ba ni tsoro da bantsoronka.
Eloignez votre main de moi, et que votre crainte ne m’épouvante pas.
22 Sa’an nan ka kira ni, zan kuwa amsa, ko kuma ka bar ni in yi magana sai ka amsa mini.
Appelez-moi, et moi je vous répondrai; ou bien je parlerai, et vous, répondez-moi.
23 Abubuwa nawa na yi waɗanda ba daidai ba, kuma zunubi ne? Ka nuna mini laifina da zunubina.
Combien ai-je d’iniquités et de péchés? Montrez-moi mes crimes et mes offenses.
24 Don me ka ɓoye mini fuskarka; ka kuma sa na zama kamar maƙiyinka?
Pourquoi me cachez-vous votre face, et me croyez-vous votre ennemi?
25 Ko za a wahalar da ganye wanda iska take hurawa? Ko za ka bi busasshiyar ciyawa?
C’est contre la feuille qui est emportée par le vent que vous montrez votre puissance, et c’est la paille desséchée que vous poursuivez;
26 Gama ka rubuta abubuwa marasa daɗi game da ni; ka sa na yi gādon zunuban ƙuruciyata.
Car vous écrivez contre moi des sentences très rigoureuses, et vous voulez me consumer pour les péchés de ma jeunesse.
27 Ka daure ƙafafuna da sarƙa; kana kallon duk inda na taka ta wurin sa shaida a tafin ƙafafuna.
Vous avez mis mes pieds dans les chaînes, vous avez observé tous mes sentiers, et vous avez considéré les traces de mes pieds;
28 “Haka mutum yake lalacewa kamar ruɓaɓɓen abu, kamar rigar da asu ya cinye.
Moi qui dois être consumé comme un objet putréfié, et comme un vêtement qui est rongé par les vers.

< Ayuba 13 >