< Ayuba 13 >

1 “Idanuna sun ga waɗannan duka, kunnuwana sun ji sun kuma gane.
Voici, mon œil a vu tout cela; mon oreille l'a entendu et compris;
2 Abin da kuka sani, ni ma na sani; ba ku fi ni ba.
Ce que vous savez, je le sais aussi; je ne vous suis pas inférieur.
3 Amma ina so in yi magana da Maɗaukaki, in kai kukana wurin Allah kai tsaye.
Mais je veux parler au Tout-Puissant, je veux plaider auprès de Dieu.
4 Ku kuma kun ishe ni da ƙarairayi; ku likitocin wofi ne, dukanku!
Mais vous, vous êtes des inventeurs de mensonges. Vous êtes tous des médecins de néant.
5 In da za ku yi shiru gaba ɗaya! Zai zama muku hikima.
Puissiez-vous demeurer dans le silence, et que ce soit là votre sagesse!
6 Ku ji gardamata yanzu; ku ji roƙon da zai fito daga bakina.
Écoutez donc ma réprimande, et soyez attentifs à la réplique de mes lèvres.
7 Za ku iya yin muguwar magana a madadin Allah? Ko za ku yi ƙarya a madadinsa?
Tiendrez-vous des discours injustes en faveur de Dieu? Et, pour le défendre, direz-vous des mensonges?
8 Ko za ku nuna masa sonkai? Ko za ku yi gardama a madadinsa?
Ferez-vous acception de personnes en sa faveur? Prétendrez-vous plaider pour Dieu?
9 In ya bincike ku zai tarar ba ku da laifi? Ko za ku iya ruɗe shi yadda za ku ruɗi mutane?
Vous en prendra-t-il bien, s'il vous sonde? Comme on trompe un homme, le tromperez-vous?
10 Ba shakka zai kwaɓe ku in kun nuna sonkai a ɓoye.
Certainement, il vous reprendra, si secrètement vous faites acception de personnes.
11 Ko ikonsa ba ya ba ku tsoro? Tsoronsa ba zai auka muku ba?
Sa majesté ne vous épouvantera-t-elle point, et sa frayeur ne tombera-t-elle pas sur vous?
12 Duk surutanku kamar toka suke; kāriyarku na yimɓu ne.
Vos réminiscences sont des sentences de cendre, vos remparts sont des remparts de boue!
13 “Ku yi shiru zan yi magana; sa’an nan abin da zai same ni yă same ni.
Taisez-vous, laissez-moi; je veux parler, et qu'il m'arrive ce qui pourra.
14 Don me na sa kaina cikin hatsari na yi kasada da raina?
Pourquoi prendrais-je ma chair dans mes dents? Non, j'exposerai ma vie.
15 Ko da zai kashe ni ne, begena a cikinsa zai kasance; ba shakka zan kāre kaina a gabansa
Voici, il me tuera; je n'ai plus d'espoir. Du moins, je défendrai ma conduite devant lui.
16 lalle wannan zai kawo mini kuɓuta gama ba wani marar tsoron Allah da zai iya zuwa wurinsa!
Et cela me tournera à salut; car un impie ne viendrait pas devant lui.
17 Ku saurara da kyau ku ji abin da zan faɗa; bari kunnuwanku su ji abin da zan ce.
Écoutez, écoutez mes paroles, prêtez l'oreille à mes déclarations.
18 Yanzu da na shirya ƙarata, na san za a ce ba ni da laifi.
Voici, j'ai préparé ma cause. Je sais que je serai justifié.
19 Ko wani zai ce ga laifin da na yi? In an same ni da laifi, zan yi shiru in mutu.
Quelqu'un plaidera-t-il contre moi? Alors je me tais, et je meurs.
20 “Kai dai biya mini waɗannan bukatu biyu kawai ya Allah, ba zan kuwa ɓoye daga gare ka ba;
Seulement, ne me fais point deux choses, et alors je ne me cacherai pas loin de ta face:
21 Ka janye hannunka nesa da ni, ka daina ba ni tsoro da bantsoronka.
Éloigne ta main de moi, et que ta terreur ne me trouble point.
22 Sa’an nan ka kira ni, zan kuwa amsa, ko kuma ka bar ni in yi magana sai ka amsa mini.
Puis, appelle-moi et je répondrai. Ou bien, que je parle, et tu me répliqueras.
23 Abubuwa nawa na yi waɗanda ba daidai ba, kuma zunubi ne? Ka nuna mini laifina da zunubina.
Combien ai-je commis d'iniquités et de péchés? Fais-moi connaître ma transgression et mon péché.
24 Don me ka ɓoye mini fuskarka; ka kuma sa na zama kamar maƙiyinka?
Pourquoi caches-tu ta face, et me tiens-tu pour ton ennemi?
25 Ko za a wahalar da ganye wanda iska take hurawa? Ko za ka bi busasshiyar ciyawa?
Veux-tu effrayer une feuille que le vent emporte, et poursuivre une paille desséchée?
26 Gama ka rubuta abubuwa marasa daɗi game da ni; ka sa na yi gādon zunuban ƙuruciyata.
Pour que tu écrives contre moi d'amers arrêts, et que tu me fasses recevoir la peine des péchés de ma jeunesse;
27 Ka daure ƙafafuna da sarƙa; kana kallon duk inda na taka ta wurin sa shaida a tafin ƙafafuna.
Pour que tu mettes mes pieds dans des ceps, que tu épies tous mes chemins, et que tu traces une limite autour de la plante de mes pieds;
28 “Haka mutum yake lalacewa kamar ruɓaɓɓen abu, kamar rigar da asu ya cinye.
Et ce corps se détruit comme du bois vermoulu, comme un vêtement que la teigne a rongé.

< Ayuba 13 >