< Ayuba 13 >

1 “Idanuna sun ga waɗannan duka, kunnuwana sun ji sun kuma gane.
Voici, mon œil a vu toutes ces choses, [et] mon oreille les a ouïes et entendues.
2 Abin da kuka sani, ni ma na sani; ba ku fi ni ba.
Comme vous les savez, je les sais aussi; je ne vous suis pas inférieur.
3 Amma ina so in yi magana da Maɗaukaki, in kai kukana wurin Allah kai tsaye.
Mais je parlerai au Tout-puissant, et je prendrai plaisir à dire mes raisons au [Dieu] Fort.
4 Ku kuma kun ishe ni da ƙarairayi; ku likitocin wofi ne, dukanku!
Et certes vous inventez des mensonges; vous êtes tous des médecins inutiles.
5 In da za ku yi shiru gaba ɗaya! Zai zama muku hikima.
Plût à Dieu que vous demeurassiez entièrement dans le silence; et cela vous serait réputé à sagesse.
6 Ku ji gardamata yanzu; ku ji roƙon da zai fito daga bakina.
Ecoutez donc maintenant mon raisonnement, et soyez attentifs à la défense de mes lèvres:
7 Za ku iya yin muguwar magana a madadin Allah? Ko za ku yi ƙarya a madadinsa?
Allégueriez-vous des choses injustes, en faveur du [Dieu] Fort, et diriez-vous quelque fausseté pour lui?
8 Ko za ku nuna masa sonkai? Ko za ku yi gardama a madadinsa?
Ferez-vous acception de sa personne, si vous plaidez la cause du [Dieu] Fort?
9 In ya bincike ku zai tarar ba ku da laifi? Ko za ku iya ruɗe shi yadda za ku ruɗi mutane?
Vous en prendra-t-il bien, s'il vous sonde? vous jouerez-vous de lui, comme on se joue d'un homme [mortel]?
10 Ba shakka zai kwaɓe ku in kun nuna sonkai a ɓoye.
Certainement il vous censurera, si même en secret vous faites acception de personnes.
11 Ko ikonsa ba ya ba ku tsoro? Tsoronsa ba zai auka muku ba?
Sa majesté ne vous épouvantera-t-elle point? et sa frayeur ne tombera-t-elle point sur vous?
12 Duk surutanku kamar toka suke; kāriyarku na yimɓu ne.
Vos discours mémorables sont des sentences de cendre, et vos éminences sont des éminences de boue.
13 “Ku yi shiru zan yi magana; sa’an nan abin da zai same ni yă same ni.
Taisez-vous devant moi, et que je parle; et qu'il m'arrive ce qui pourra.
14 Don me na sa kaina cikin hatsari na yi kasada da raina?
Pourquoi porté-je ma chair entre mes dents, et tiens-je mon âme entre mes mains?
15 Ko da zai kashe ni ne, begena a cikinsa zai kasance; ba shakka zan kāre kaina a gabansa
Voilà, qu'il me tue, je ne laisserai pas d'espérer [en lui]; et je défendrai ma conduite en sa présence.
16 lalle wannan zai kawo mini kuɓuta gama ba wani marar tsoron Allah da zai iya zuwa wurinsa!
Et qui plus est, il sera lui-même ma délivrance; mais l'hypocrite ne viendra point devant sa face.
17 Ku saurara da kyau ku ji abin da zan faɗa; bari kunnuwanku su ji abin da zan ce.
Ecoutez attentivement mes discours, et prêtez l'oreille à ce que je vais vous déclarer.
18 Yanzu da na shirya ƙarata, na san za a ce ba ni da laifi.
Voilà, aussitôt que j'aurai déduit par ordre mon droit, je sais que je serai justifié.
19 Ko wani zai ce ga laifin da na yi? In an same ni da laifi, zan yi shiru in mutu.
Qui est-ce qui veut disputer contre moi? car maintenant si je me tais, je mourrai.
20 “Kai dai biya mini waɗannan bukatu biyu kawai ya Allah, ba zan kuwa ɓoye daga gare ka ba;
Seulement ne me fais point ces deux choses, [et] alors je ne me cacherai point devant ta face;
21 Ka janye hannunka nesa da ni, ka daina ba ni tsoro da bantsoronka.
Retire ta main de dessus moi, et que ta frayeur ne me trouble point.
22 Sa’an nan ka kira ni, zan kuwa amsa, ko kuma ka bar ni in yi magana sai ka amsa mini.
Puis appelle-moi, et je répondrai; ou bien je parlerai, et tu me répondras.
23 Abubuwa nawa na yi waɗanda ba daidai ba, kuma zunubi ne? Ka nuna mini laifina da zunubina.
Combien ai-je d'iniquités et de péchés? Montre-moi mon crime et mon péché.
24 Don me ka ɓoye mini fuskarka; ka kuma sa na zama kamar maƙiyinka?
Pourquoi caches-tu ta face, et me tiens-tu pour ton ennemi?
25 Ko za a wahalar da ganye wanda iska take hurawa? Ko za ka bi busasshiyar ciyawa?
Déploieras-tu tes forces contre une feuille que le vent emporte? poursuivras-tu du chaume tout sec?
26 Gama ka rubuta abubuwa marasa daɗi game da ni; ka sa na yi gādon zunuban ƙuruciyata.
Que tu donnes contre moi des arrêts d'amertume, et que tu me fasses porter la peine des péchés de ma jeunesse?
27 Ka daure ƙafafuna da sarƙa; kana kallon duk inda na taka ta wurin sa shaida a tafin ƙafafuna.
Et que tu mettes mes pieds aux ceps, et observes tous mes chemins? et que tu suives les traces de mes pieds?
28 “Haka mutum yake lalacewa kamar ruɓaɓɓen abu, kamar rigar da asu ya cinye.
Car celui [que tu poursuis de cette manière, ] s'en va par pièces comme du bois vermoulu, et comme une robe que la teigne a rongée.

< Ayuba 13 >