< Ayuba 13 >

1 “Idanuna sun ga waɗannan duka, kunnuwana sun ji sun kuma gane.
Lo! all this mine eye hath seen; Mine ear hath heard and understood it.
2 Abin da kuka sani, ni ma na sani; ba ku fi ni ba.
What ye know, I know also; I am not inferior to you.
3 Amma ina so in yi magana da Maɗaukaki, in kai kukana wurin Allah kai tsaye.
But O that I might speak with the Almighty! O that I might reason with God!
4 Ku kuma kun ishe ni da ƙarairayi; ku likitocin wofi ne, dukanku!
For ye are forgers of lies; Physicians of no value, all of you!
5 In da za ku yi shiru gaba ɗaya! Zai zama muku hikima.
O that ye would altogether hold your peace! This, truly, would be wisdom in you.
6 Ku ji gardamata yanzu; ku ji roƙon da zai fito daga bakina.
Hear, I pray you, my arguments; Attend to the pleadings of my lips!
7 Za ku iya yin muguwar magana a madadin Allah? Ko za ku yi ƙarya a madadinsa?
Will ye speak falsehood for God? Will ye utter deceit for him?
8 Ko za ku nuna masa sonkai? Ko za ku yi gardama a madadinsa?
Will ye be partial to his person? Will ye contend earnestly for God?
9 In ya bincike ku zai tarar ba ku da laifi? Ko za ku iya ruɗe shi yadda za ku ruɗi mutane?
Will it be well for you, if he search you thoroughly? Can ye deceive him, as one may deceive a man?
10 Ba shakka zai kwaɓe ku in kun nuna sonkai a ɓoye.
Surely he will rebuke you, If ye secretly have respect to persons.
11 Ko ikonsa ba ya ba ku tsoro? Tsoronsa ba zai auka muku ba?
Doth not his majesty make you afraid, And his dread fall upon you?
12 Duk surutanku kamar toka suke; kāriyarku na yimɓu ne.
Your maxims are words of dust; Your fortresses are fortresses of clay.
13 “Ku yi shiru zan yi magana; sa’an nan abin da zai same ni yă same ni.
Hold your peace, and let me speak: And then come upon me what will!
14 Don me na sa kaina cikin hatsari na yi kasada da raina?
Why do I take my flesh in my teeth, And put my life in my hand?
15 Ko da zai kashe ni ne, begena a cikinsa zai kasance; ba shakka zan kāre kaina a gabansa
Lo! he slayeth me, and I have no hope! Yet will I justify my ways before him.
16 lalle wannan zai kawo mini kuɓuta gama ba wani marar tsoron Allah da zai iya zuwa wurinsa!
This also shall be my deliverance; For no unrighteous man will come before him.
17 Ku saurara da kyau ku ji abin da zan faɗa; bari kunnuwanku su ji abin da zan ce.
Hear attentively my words, And give ear to my declaration!
18 Yanzu da na shirya ƙarata, na san za a ce ba ni da laifi.
Behold, I have now set in order my cause; I know that I am innocent.
19 Ko wani zai ce ga laifin da na yi? In an same ni da laifi, zan yi shiru in mutu.
Who is he that can contend with me? For then would I hold my peace, and die!
20 “Kai dai biya mini waɗannan bukatu biyu kawai ya Allah, ba zan kuwa ɓoye daga gare ka ba;
Only do not unto me two things, Then will I not hide myself from thy presence;
21 Ka janye hannunka nesa da ni, ka daina ba ni tsoro da bantsoronka.
Let not thy hand be heavy upon me, And let not thy terrors make me afraid:
22 Sa’an nan ka kira ni, zan kuwa amsa, ko kuma ka bar ni in yi magana sai ka amsa mini.
Then call upon me, and I will answer; Or I will speak, and answer thou me.
23 Abubuwa nawa na yi waɗanda ba daidai ba, kuma zunubi ne? Ka nuna mini laifina da zunubina.
How many are my iniquities and sins? Make me to know my faults and transgressions.
24 Don me ka ɓoye mini fuskarka; ka kuma sa na zama kamar maƙiyinka?
Wherefore dost thou hide thy face, And account me as thine enemy?
25 Ko za a wahalar da ganye wanda iska take hurawa? Ko za ka bi busasshiyar ciyawa?
Wilt thou put in fear the driven leaf? Wilt thou pursue the dry stubble?
26 Gama ka rubuta abubuwa marasa daɗi game da ni; ka sa na yi gādon zunuban ƙuruciyata.
For thou writest bitter things against me, And makest me inherit the sins of my youth.
27 Ka daure ƙafafuna da sarƙa; kana kallon duk inda na taka ta wurin sa shaida a tafin ƙafafuna.
Yea, thou puttest my feet in the stocks, And waterest all my paths; Thou hemmest in the soles of my feet.
28 “Haka mutum yake lalacewa kamar ruɓaɓɓen abu, kamar rigar da asu ya cinye.
And I, like an abandoned thing, shall waste away; Like a garment which is moth-eaten.

< Ayuba 13 >