< Ayuba 13 >

1 “Idanuna sun ga waɗannan duka, kunnuwana sun ji sun kuma gane.
Lo, mine eye hath seen all this, mine ear hath heard and understood it.
2 Abin da kuka sani, ni ma na sani; ba ku fi ni ba.
What ye know, the same do I know also: I am not inferior unto you.
3 Amma ina so in yi magana da Maɗaukaki, in kai kukana wurin Allah kai tsaye.
Surely I would speak to the Almighty, and I desire to reason with God.
4 Ku kuma kun ishe ni da ƙarairayi; ku likitocin wofi ne, dukanku!
But ye are forgers of lies, ye are all physicians of no value.
5 In da za ku yi shiru gaba ɗaya! Zai zama muku hikima.
O that ye would altogether hold your peace! and it should be your wisdom.
6 Ku ji gardamata yanzu; ku ji roƙon da zai fito daga bakina.
Hear now my reasoning, and hearken to the pleadings of my lips.
7 Za ku iya yin muguwar magana a madadin Allah? Ko za ku yi ƙarya a madadinsa?
Will ye speak wickedly for God? and talk deceitfully for him?
8 Ko za ku nuna masa sonkai? Ko za ku yi gardama a madadinsa?
Will ye accept his person? will ye contend for God?
9 In ya bincike ku zai tarar ba ku da laifi? Ko za ku iya ruɗe shi yadda za ku ruɗi mutane?
Is it good that he should search you out? or as one man mocketh another, do ye so mock him?
10 Ba shakka zai kwaɓe ku in kun nuna sonkai a ɓoye.
He will surely reprove you, if ye do secretly accept persons.
11 Ko ikonsa ba ya ba ku tsoro? Tsoronsa ba zai auka muku ba?
Shall not his excellency make you afraid? and his dread fall upon you?
12 Duk surutanku kamar toka suke; kāriyarku na yimɓu ne.
Your remembrances are like unto ashes, your bodies to bodies of clay.
13 “Ku yi shiru zan yi magana; sa’an nan abin da zai same ni yă same ni.
Hold your peace, let me alone, that I may speak, and let come on me what will.
14 Don me na sa kaina cikin hatsari na yi kasada da raina?
Wherefore do I take my flesh in my teeth, and put my life in mine hand?
15 Ko da zai kashe ni ne, begena a cikinsa zai kasance; ba shakka zan kāre kaina a gabansa
Though he slay me, yet will I trust in him: but I will maintain mine own ways before him.
16 lalle wannan zai kawo mini kuɓuta gama ba wani marar tsoron Allah da zai iya zuwa wurinsa!
He also shall be my salvation: for an hypocrite shall not come before him.
17 Ku saurara da kyau ku ji abin da zan faɗa; bari kunnuwanku su ji abin da zan ce.
Hear diligently my speech, and my declaration with your ears.
18 Yanzu da na shirya ƙarata, na san za a ce ba ni da laifi.
Behold now, I have ordered my cause; I know that I shall be justified.
19 Ko wani zai ce ga laifin da na yi? In an same ni da laifi, zan yi shiru in mutu.
Who is he that will plead with me? for now, if I hold my tongue, I shall give up the ghost.
20 “Kai dai biya mini waɗannan bukatu biyu kawai ya Allah, ba zan kuwa ɓoye daga gare ka ba;
Only do not two things unto me: then will I not hide myself from thee.
21 Ka janye hannunka nesa da ni, ka daina ba ni tsoro da bantsoronka.
Withdraw thine hand far from me: and let not thy dread make me afraid.
22 Sa’an nan ka kira ni, zan kuwa amsa, ko kuma ka bar ni in yi magana sai ka amsa mini.
Then call thou, and I will answer: or let me speak, and answer thou me.
23 Abubuwa nawa na yi waɗanda ba daidai ba, kuma zunubi ne? Ka nuna mini laifina da zunubina.
How many are mine iniquities and sins? make me to know my transgression and my sin.
24 Don me ka ɓoye mini fuskarka; ka kuma sa na zama kamar maƙiyinka?
Wherefore hidest thou thy face, and holdest me for thine enemy?
25 Ko za a wahalar da ganye wanda iska take hurawa? Ko za ka bi busasshiyar ciyawa?
Wilt thou break a leaf driven to and fro? and wilt thou pursue the dry stubble?
26 Gama ka rubuta abubuwa marasa daɗi game da ni; ka sa na yi gādon zunuban ƙuruciyata.
For thou writest bitter things against me, and makest me to possess the iniquities of my youth.
27 Ka daure ƙafafuna da sarƙa; kana kallon duk inda na taka ta wurin sa shaida a tafin ƙafafuna.
Thou puttest my feet also in the stocks, and lookest narrowly unto all my paths; thou settest a print upon the heels of my feet.
28 “Haka mutum yake lalacewa kamar ruɓaɓɓen abu, kamar rigar da asu ya cinye.
And he, as a rotten thing, consumeth, as a garment that is moth eaten.

< Ayuba 13 >