< Ayuba 13 >
1 “Idanuna sun ga waɗannan duka, kunnuwana sun ji sun kuma gane.
Lo, mine eye hath seen all [this], mine ear hath heard and understood it.
2 Abin da kuka sani, ni ma na sani; ba ku fi ni ba.
What ye know, I know also: I am not inferior to you.
3 Amma ina so in yi magana da Maɗaukaki, in kai kukana wurin Allah kai tsaye.
But I will speak to the Almighty, and will find pleasure in reasoning with God;
4 Ku kuma kun ishe ni da ƙarairayi; ku likitocin wofi ne, dukanku!
For ye indeed are forgers of lies, ye are all physicians of no value.
5 In da za ku yi shiru gaba ɗaya! Zai zama muku hikima.
Oh that ye would be altogether silent! and it would be your wisdom.
6 Ku ji gardamata yanzu; ku ji roƙon da zai fito daga bakina.
Hear now my defence, and hearken to the pleadings of my lips.
7 Za ku iya yin muguwar magana a madadin Allah? Ko za ku yi ƙarya a madadinsa?
Will ye speak unrighteously for God? and for him speak deceit?
8 Ko za ku nuna masa sonkai? Ko za ku yi gardama a madadinsa?
Will ye accept his person? will ye contend for God?
9 In ya bincike ku zai tarar ba ku da laifi? Ko za ku iya ruɗe shi yadda za ku ruɗi mutane?
Will it be well if he should search you out? or as one mocketh at a man, will ye mock at him?
10 Ba shakka zai kwaɓe ku in kun nuna sonkai a ɓoye.
He will certainly reprove you, if ye do secretly accept persons.
11 Ko ikonsa ba ya ba ku tsoro? Tsoronsa ba zai auka muku ba?
Shall not his excellency terrify you? and his dread fall upon you?
12 Duk surutanku kamar toka suke; kāriyarku na yimɓu ne.
Your memorable sayings are proverbs of ashes, your bulwarks are bulwarks of mire.
13 “Ku yi shiru zan yi magana; sa’an nan abin da zai same ni yă same ni.
Hold your peace from me, and I will speak, and let come on me what [will]!
14 Don me na sa kaina cikin hatsari na yi kasada da raina?
Wherefore should I take my flesh in my teeth, and put my life in my hand?
15 Ko da zai kashe ni ne, begena a cikinsa zai kasance; ba shakka zan kāre kaina a gabansa
Behold, if he slay me, yet would I trust in him; but I will defend mine own ways before him.
16 lalle wannan zai kawo mini kuɓuta gama ba wani marar tsoron Allah da zai iya zuwa wurinsa!
This also shall be my salvation, that a profane man shall not come before his face.
17 Ku saurara da kyau ku ji abin da zan faɗa; bari kunnuwanku su ji abin da zan ce.
Hear attentively my speech and my declaration with your ears.
18 Yanzu da na shirya ƙarata, na san za a ce ba ni da laifi.
Behold now, I have ordered the cause; I know that I shall be justified.
19 Ko wani zai ce ga laifin da na yi? In an same ni da laifi, zan yi shiru in mutu.
Who is he that contendeth with me? For if I were silent now, I should expire.
20 “Kai dai biya mini waɗannan bukatu biyu kawai ya Allah, ba zan kuwa ɓoye daga gare ka ba;
Only do not two things unto me; then will I not hide myself from thee.
21 Ka janye hannunka nesa da ni, ka daina ba ni tsoro da bantsoronka.
Withdraw thy hand far from me; and let not thy terror make me afraid:
22 Sa’an nan ka kira ni, zan kuwa amsa, ko kuma ka bar ni in yi magana sai ka amsa mini.
Then call, and I will answer; or I will speak, and answer thou me.
23 Abubuwa nawa na yi waɗanda ba daidai ba, kuma zunubi ne? Ka nuna mini laifina da zunubina.
How many are mine iniquities and sins? Make me to know my transgression and my sin.
24 Don me ka ɓoye mini fuskarka; ka kuma sa na zama kamar maƙiyinka?
Wherefore dost thou hide thy face, and countest me for thine enemy?
25 Ko za a wahalar da ganye wanda iska take hurawa? Ko za ka bi busasshiyar ciyawa?
Wilt thou terrify a driven leaf? and wilt thou pursue dry stubble?
26 Gama ka rubuta abubuwa marasa daɗi game da ni; ka sa na yi gādon zunuban ƙuruciyata.
For thou writest bitter things against me, and makest me to possess the iniquities of my youth;
27 Ka daure ƙafafuna da sarƙa; kana kallon duk inda na taka ta wurin sa shaida a tafin ƙafafuna.
And thou puttest my feet in the stocks, and markest all my paths; thou settest a bound about the soles of my feet; —
28 “Haka mutum yake lalacewa kamar ruɓaɓɓen abu, kamar rigar da asu ya cinye.
One who, as a rotten thing consumeth, as a garment that the moth eateth.