< Ayuba 13 >
1 “Idanuna sun ga waɗannan duka, kunnuwana sun ji sun kuma gane.
Lo, my eye has seen all this. My ear has heard and understood it.
2 Abin da kuka sani, ni ma na sani; ba ku fi ni ba.
What ye know, I also know; I am not inferior to you.
3 Amma ina so in yi magana da Maɗaukaki, in kai kukana wurin Allah kai tsaye.
Surely I would speak to the Almighty, and I desire to reason with God.
4 Ku kuma kun ishe ni da ƙarairayi; ku likitocin wofi ne, dukanku!
But ye are forgers of lies. Ye are all physicians of no value.
5 In da za ku yi shiru gaba ɗaya! Zai zama muku hikima.
O that ye would altogether be silent! And it would be your wisdom.
6 Ku ji gardamata yanzu; ku ji roƙon da zai fito daga bakina.
Hear now my reasoning, and hearken to the pleadings of my lips.
7 Za ku iya yin muguwar magana a madadin Allah? Ko za ku yi ƙarya a madadinsa?
Will ye speak unrighteously for God, and talk deceitfully for him?
8 Ko za ku nuna masa sonkai? Ko za ku yi gardama a madadinsa?
Will ye show partiality to him? Will ye contend for God?
9 In ya bincike ku zai tarar ba ku da laifi? Ko za ku iya ruɗe shi yadda za ku ruɗi mutane?
Is it good that he should search you out? Or as deceiving a man, will ye deceive him?
10 Ba shakka zai kwaɓe ku in kun nuna sonkai a ɓoye.
He will surely reprove you if ye secretly show partiality.
11 Ko ikonsa ba ya ba ku tsoro? Tsoronsa ba zai auka muku ba?
Shall not his majesty make you afraid, and his dread fall upon you?
12 Duk surutanku kamar toka suke; kāriyarku na yimɓu ne.
Your memorable sayings are proverbs of ashes. Your defenses are defenses of clay.
13 “Ku yi shiru zan yi magana; sa’an nan abin da zai same ni yă same ni.
Be quiet. Let me alone that I may speak, and let come on me what will.
14 Don me na sa kaina cikin hatsari na yi kasada da raina?
Why should I take my flesh in my teeth, and put my life in my hand?
15 Ko da zai kashe ni ne, begena a cikinsa zai kasance; ba shakka zan kāre kaina a gabansa
Behold, he will kill me; I have no hope. Nevertheless I will maintain my ways before him.
16 lalle wannan zai kawo mini kuɓuta gama ba wani marar tsoron Allah da zai iya zuwa wurinsa!
This also shall be my salvation, that a profane man shall not come before him.
17 Ku saurara da kyau ku ji abin da zan faɗa; bari kunnuwanku su ji abin da zan ce.
Hear diligently my speech, and let my declaration be in your ears.
18 Yanzu da na shirya ƙarata, na san za a ce ba ni da laifi.
Behold now, I have set my case in order. I know that I am righteous.
19 Ko wani zai ce ga laifin da na yi? In an same ni da laifi, zan yi shiru in mutu.
Who is he who will contend with me? For then I would keep silent and give up the spirit.
20 “Kai dai biya mini waɗannan bukatu biyu kawai ya Allah, ba zan kuwa ɓoye daga gare ka ba;
Only do not do two things to me, then I will not hide myself from thy face:
21 Ka janye hannunka nesa da ni, ka daina ba ni tsoro da bantsoronka.
Withdraw thy hand far from me, and do not let thy dread make me afraid.
22 Sa’an nan ka kira ni, zan kuwa amsa, ko kuma ka bar ni in yi magana sai ka amsa mini.
Then call thou, and I will answer, or let me speak, and answer thou me.
23 Abubuwa nawa na yi waɗanda ba daidai ba, kuma zunubi ne? Ka nuna mini laifina da zunubina.
How many are my iniquities and sins? Make me to know my transgression and my sin.
24 Don me ka ɓoye mini fuskarka; ka kuma sa na zama kamar maƙiyinka?
Why do thou hide thy face, and reckon me for thine enemy?
25 Ko za a wahalar da ganye wanda iska take hurawa? Ko za ka bi busasshiyar ciyawa?
Will thou harass a driven leaf? And will thou pursue the dry stubble?
26 Gama ka rubuta abubuwa marasa daɗi game da ni; ka sa na yi gādon zunuban ƙuruciyata.
For thou write bitter things against me, and make me to inherit the iniquities of my youth.
27 Ka daure ƙafafuna da sarƙa; kana kallon duk inda na taka ta wurin sa shaida a tafin ƙafafuna.
Thou also put my feet in the stocks, and mark all my paths. Thou set a bound to the soles of my feet.
28 “Haka mutum yake lalacewa kamar ruɓaɓɓen abu, kamar rigar da asu ya cinye.
Though I am like a rotten thing that decays, like a garment that is moth-eaten.