< Ayuba 13 >

1 “Idanuna sun ga waɗannan duka, kunnuwana sun ji sun kuma gane.
Se, mit Øje har skuet alt dette, mit Øre har hørt og mærket sig det;
2 Abin da kuka sani, ni ma na sani; ba ku fi ni ba.
hvad I ved, ved også jeg, jeg falder ikke igennem for jer.
3 Amma ina so in yi magana da Maɗaukaki, in kai kukana wurin Allah kai tsaye.
Men til den Almægtige vil jeg tale, med Gud er jeg sindet at gå i Rette,
4 Ku kuma kun ishe ni da ƙarairayi; ku likitocin wofi ne, dukanku!
mens I smører på med Løgn; usle Læger er I til Hobe.
5 In da za ku yi shiru gaba ɗaya! Zai zama muku hikima.
Om I dog vilde tie stille, så kunde I regnes for vise!
6 Ku ji gardamata yanzu; ku ji roƙon da zai fito daga bakina.
Hør dog mit Klagemål, mærk mine Læbers Anklage!
7 Za ku iya yin muguwar magana a madadin Allah? Ko za ku yi ƙarya a madadinsa?
Forsvarer I Gud med Uret, forsvarer I ham med Svig?
8 Ko za ku nuna masa sonkai? Ko za ku yi gardama a madadinsa?
Vil I tage Parti for ham, vil I træde i Skranken for Gud?
9 In ya bincike ku zai tarar ba ku da laifi? Ko za ku iya ruɗe shi yadda za ku ruɗi mutane?
Går det godt, når han ransager eder, kan I narre ham, som man narrer et Menneske?
10 Ba shakka zai kwaɓe ku in kun nuna sonkai a ɓoye.
Revse jer vil han alvorligt, om I lader som intet og dog er partiske.
11 Ko ikonsa ba ya ba ku tsoro? Tsoronsa ba zai auka muku ba?
Vil ikke hans Højhed skræmme jer og hans Rædsel falde på eder?
12 Duk surutanku kamar toka suke; kāriyarku na yimɓu ne.
Eders Tankesprog bliver til Askesprog, som Skjolde af Ler eders Skjolde.
13 “Ku yi shiru zan yi magana; sa’an nan abin da zai same ni yă same ni.
Ti stille, at jeg kan tale, så overgå mig, hvad der vil!
14 Don me na sa kaina cikin hatsari na yi kasada da raina?
Jeg vil bære mit Kød i Tænderne og tage mit Liv i min Hånd;
15 Ko da zai kashe ni ne, begena a cikinsa zai kasance; ba shakka zan kāre kaina a gabansa
se, han slår mig ihjel, jeg har intet Håb, dog lægger jeg for ham min Færd.
16 lalle wannan zai kawo mini kuɓuta gama ba wani marar tsoron Allah da zai iya zuwa wurinsa!
Det er i sig selv en Sejr for mig, thi en vanhellig vover sig ikke til ham!
17 Ku saurara da kyau ku ji abin da zan faɗa; bari kunnuwanku su ji abin da zan ce.
Hør nu ret på mit Ord, lad mig tale for eders Ører!
18 Yanzu da na shirya ƙarata, na san za a ce ba ni da laifi.
Se, til Rettergang er jeg rede, jeg ved, at Retten er min!
19 Ko wani zai ce ga laifin da na yi? In an same ni da laifi, zan yi shiru in mutu.
Hvem kan vel trætte med mig? Da skulde jeg tie og opgive Ånden!
20 “Kai dai biya mini waɗannan bukatu biyu kawai ya Allah, ba zan kuwa ɓoye daga gare ka ba;
Kun for to Ting skåne du mig, så kryber jeg ikke i Skjul for dig:
21 Ka janye hannunka nesa da ni, ka daina ba ni tsoro da bantsoronka.
Din Hånd må du tage fra mig, din Rædsel skræmme mig ikke!
22 Sa’an nan ka kira ni, zan kuwa amsa, ko kuma ka bar ni in yi magana sai ka amsa mini.
Så stævn mig, og jeg skal svare, eller jeg vil tale, og du skal svare!
23 Abubuwa nawa na yi waɗanda ba daidai ba, kuma zunubi ne? Ka nuna mini laifina da zunubina.
Hvor stor er min Skyld og Synd? Lad mig vide min Brøde og Synd!
24 Don me ka ɓoye mini fuskarka; ka kuma sa na zama kamar maƙiyinka?
Hvi skjuler du dog dit Åsyn og regner mig for din Fjende?
25 Ko za a wahalar da ganye wanda iska take hurawa? Ko za ka bi busasshiyar ciyawa?
Vil du skræmme et henvejret Blad, forfølge et vissent Strå,
26 Gama ka rubuta abubuwa marasa daɗi game da ni; ka sa na yi gādon zunuban ƙuruciyata.
at du skriver mig så bitter en Dom og lader mig arve min Ungdoms Skyld,
27 Ka daure ƙafafuna da sarƙa; kana kallon duk inda na taka ta wurin sa shaida a tafin ƙafafuna.
lægger mine Fødder i Blokken, vogter på alle mine Veje. indkredser mine Fødders Trin!
28 “Haka mutum yake lalacewa kamar ruɓaɓɓen abu, kamar rigar da asu ya cinye.
Og så er han dog som smuldrende Trøske, som Klæder, der ædes op af Møl,

< Ayuba 13 >