< Ayuba 13 >
1 “Idanuna sun ga waɗannan duka, kunnuwana sun ji sun kuma gane.
Aj, všecko to vidělo oko mé, slyšelo ucho mé, a srozumělo tomu.
2 Abin da kuka sani, ni ma na sani; ba ku fi ni ba.
Jakož vy znáte to, znám i já, nejsem zpozdilejší než vy.
3 Amma ina so in yi magana da Maɗaukaki, in kai kukana wurin Allah kai tsaye.
Jistě žeť já s Všemohoucím mluviti, a s Bohem silným o svou při jednati budu.
4 Ku kuma kun ishe ni da ƙarairayi; ku likitocin wofi ne, dukanku!
Nebo vy jste skladatelé lži, a lékaři marní všickni vy.
5 In da za ku yi shiru gaba ɗaya! Zai zama muku hikima.
Ó kdybyste aspoň mlčeli, a bylo by vám to za moudrost.
6 Ku ji gardamata yanzu; ku ji roƙon da zai fito daga bakina.
Slyštež medle odpory mé, a důvodů rtů mých pozorujte.
7 Za ku iya yin muguwar magana a madadin Allah? Ko za ku yi ƙarya a madadinsa?
Zdali zastávajíce Boha silného, mluviti máte nepravost? Aneb za něho mluviti máte lest?
8 Ko za ku nuna masa sonkai? Ko za ku yi gardama a madadinsa?
Zdaliž osobu jeho přijímati budete, a o Boha silného se zasazovati?
9 In ya bincike ku zai tarar ba ku da laifi? Ko za ku iya ruɗe shi yadda za ku ruɗi mutane?
Zdaž vám to k dobrému bude, když na průbu vezme vás, že jakož člověk oklamán bývá, oklamati jej chcete?
10 Ba shakka zai kwaɓe ku in kun nuna sonkai a ɓoye.
V pravdě žeť vám přísně domlouvati bude, budete-li povrchně osoby jeho šetřiti.
11 Ko ikonsa ba ya ba ku tsoro? Tsoronsa ba zai auka muku ba?
Což ani důstojnost jeho vás nepředěšuje, ani strach jeho nepřikvačuje vás?
12 Duk surutanku kamar toka suke; kāriyarku na yimɓu ne.
Všecka vzácnost vaše podobná jest popelu, a hromadám bláta vyvýšení vaše.
13 “Ku yi shiru zan yi magana; sa’an nan abin da zai same ni yă same ni.
Postrptež mne, nechať já mluvím, přiď na mne cokoli.
14 Don me na sa kaina cikin hatsari na yi kasada da raina?
Pročež bych trhati měl maso své zuby svými, a duši svou klásti v ruku svou?
15 Ko da zai kashe ni ne, begena a cikinsa zai kasance; ba shakka zan kāre kaina a gabansa
By mne i zabil, což bych v něho nedoufal? A však cesty své před oblíčej jeho předložím.
16 lalle wannan zai kawo mini kuɓuta gama ba wani marar tsoron Allah da zai iya zuwa wurinsa!
Onť sám jest spasení mé; nebo před oblíčej jeho pokrytec nepřijde.
17 Ku saurara da kyau ku ji abin da zan faɗa; bari kunnuwanku su ji abin da zan ce.
Poslouchejte pilně řeči mé, a zprávu mou pusťte v uši své.
18 Yanzu da na shirya ƙarata, na san za a ce ba ni da laifi.
Aj, jižť začínám pře své vésti, vím, že zůstanu spravedliv.
19 Ko wani zai ce ga laifin da na yi? In an same ni da laifi, zan yi shiru in mutu.
Kdo jest, ješto by mi odpíral, tak abych nyní umlknouti a umříti musil?
20 “Kai dai biya mini waɗannan bukatu biyu kawai ya Allah, ba zan kuwa ɓoye daga gare ka ba;
Toliko té dvoji věci, ó Bože, nečiň mi, a tehdy před tváří tvou nebudu se skrývati:
21 Ka janye hannunka nesa da ni, ka daina ba ni tsoro da bantsoronka.
Ruku svou vzdal ode mne, a hrůza tvá nechť mne neděsí.
22 Sa’an nan ka kira ni, zan kuwa amsa, ko kuma ka bar ni in yi magana sai ka amsa mini.
Zatím povolej mne, a buduť odpovídati; aneb nechať já mluvím, a odpovídej mi.
23 Abubuwa nawa na yi waɗanda ba daidai ba, kuma zunubi ne? Ka nuna mini laifina da zunubina.
Jak mnoho jest mých nepravostí a hříchů? Přestoupení mé a hřích můj ukaž mi.
24 Don me ka ɓoye mini fuskarka; ka kuma sa na zama kamar maƙiyinka?
Proč tvář svou skrýváš, a pokládáš mne sobě za nepřítele?
25 Ko za a wahalar da ganye wanda iska take hurawa? Ko za ka bi busasshiyar ciyawa?
Zdaliž list větrem se zmítající potříti chceš, a stéblo suché stihati budeš?
26 Gama ka rubuta abubuwa marasa daɗi game da ni; ka sa na yi gādon zunuban ƙuruciyata.
Že zapisuješ proti mně hořkosti, a dáváš mi v dědictví nepravosti mladosti mé,
27 Ka daure ƙafafuna da sarƙa; kana kallon duk inda na taka ta wurin sa shaida a tafin ƙafafuna.
A dáváš do klady nohy mé, a šetříš všech stezek mých, na paty noh mých našlapuješ;
28 “Haka mutum yake lalacewa kamar ruɓaɓɓen abu, kamar rigar da asu ya cinye.
Ješto člověk jako hnis kazí se, a jako roucho, kteréž jí mol.