< Ayuba 12 >
Därefter tog Job till orda och sade:
2 “Ba shakka ku ne mutanen nan, hikima za tă mutu tare da ku!
Ja, visst ären I det rätta folket, och med eder kommer visheten att dö ut!
3 Amma ni ma ina da hankali kamar ku; ba ku fi ni ba. Wane ne bai san duk waɗannan abubuwan ba?
Dock, jämväl jag har förstånd så gott som I, icke står jag tillbaka för eder; ty vem är den som ej begriper slikt?
4 “Na zama abin dariya ga abokaina, ko da yake na yi kira ga Allah ya kuwa amsa mini, duk da haka suka yi mini riya ko da yake ni mai adalci ne kuma marar laifi!
Så måste jag då vara ett åtlöje för min vän, jag som fick svar, så snart jag ropade till Gud; man ler åt en som är rättfärdig och ostrafflig!
5 Mutanen da ba su da damuwa suna jin daɗin ganin waɗanda suke dab da fāɗuwa.
Ja, med förakt ses olyckan av den som står säker; förakt väntar dem vilkas fötter vackla.
6 Amma wurin zaman’yan fashi yana nan ba mai damunsu, waɗanda kuma suke saɓa wa Allah suna zamansu lafiya, har ma da masu ɗaukar allahnsu a hannuwansu.
Men förhärjares hyddor åtnjuta frid, och trygghet få sådana som trotsa Gud, de som hava sin gud i sin hand.
7 “Amma ka tambayi dabbobi, za su kuma koya maka, ko kuma tsuntsayen sararin sama kuma za su gaya maka.
Men fråga du boskapen, den må undervisa dig, och fåglarna under himmelen, de må upplysa dig;
8 Ko ka yi magana da duniya, za tă kuma koya maka, ko kuma ka bar kifin teku su sanar da kai.
eller tala till jorden, hon må undervisa dig, fiskarna i havet må giva dig besked.
9 Wane ne cikin waɗannan bai san cewa hannun Ubangiji ne ya yi wannan ba?
Vem kan icke lära genom allt detta att det är HERRENS hand som har gjort det?
10 Ran kowace halitta yana a hannunsa, haka kuma numfashin dukan’yan adam.
I hans han är ju allt levandes själ och alla mänskliga varelsers anda.
11 Ko kunne ba ya gwada kalmomi kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci?
Skall icke öra pröva orden, likasom munnen prövar matens smak?
12 Ko ba a wurin tsofaffi ake samun hikima ba? Ba tsawon rai yana kawo ganewa ba?
Vishet tillkommer ju de gamle och förstånd dem som länge hava levat.
13 “Allah ne mai iko da kuma hikima, shawara da ganewa nasa ne.
Hos Honom finnes vishet och makt, hos honom råd och förstånd.
14 Abin da ya rushe ba a iya ginawa ba; in ya kulle mutum ba a iya buɗe shi a sake shi ba.
Se, vad han river ned, det bygges ej upp; för den han spärrar inne kan ingen upplåta.
15 Idan ya hana ruwan sama, za a yi fări; in kuma ya saki ruwa za a yi ambaliya.
Han håller vattnen tillbaka -- se, se då bliver där torrt, han släpper dem lösa, då fördärva de landet.
16 Shi ne mai ƙarfi da kuma mai nasara; mai ruɗi da wanda aka ruɗa, duk nasa ne.
Hos honom är kraft och klokhet, den förvillade och förvillaren äro båda i hans hand.
17 Yakan sa mashawarta su zama marasa hikima yă kuma sa wawaye su zama masu shari’a.
Rådsherrar utblottar han, han för dem i landsflykt, och domare gör han till dårar.
18 Yana cire sarƙar da sarakuna suka ɗaura yă kuma ɗaura musu wata tsumma a kwankwaso.
Han upplöser konungars välde och sätter fångbälte om deras höfter.
19 Yakan ƙasƙantar da firistoci yă kuma tumɓuke masu ikon da aka kafa tun da daɗewa.
Präster utblottar han, han för dem i landsflykt, och de säkrast rotade kommer han på fall.
20 Yana sa amintattun mashawarta su yi shiru yakan kawar da hikimar dattawa.
Välbetrodda män berövar han målet och avhänder de äldste deras insikt.
21 Yakan sa masu iko su ji kunya yă kuma ƙwace ƙarfin masu ƙarfi.
Han utgjuter förakt över furstar och lossar de starkes gördel.
22 Yana buɗe abubuwan da suke cikin duhu yă kuma kawo haske a wuraren da ba haske;
Han blottar djupen, så att de ej höljas av mörker, dödsskuggan drager han fram i ljuset.
23 yana sa al’ummai su zama manya, sai kuma yă hallaka su; yana sa al’ummai su ƙasaita, yă kuma watsar da su.
Han låter folkslag växa till -- och förgör dem; han utvidgar deras gränser, men för dem sedan bort.
24 Yana hana shugabannin duniya ganewa; Ya bar su su yi ta makuwa, su ruɗe, su ɓata.
Stamhövdingar i landet berövar han förståndet, han leder dem vilse i väglösa ödemarker.
25 Suna lallube cikin duhu ba haske; yă sa su yi ta tangaɗi kamar bugaggu.
De famla i mörkret och hava intet ljus, han kommer dem att ragla såsom druckna.