< Ayuba 12 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Y Job respondió y dijo:
2 “Ba shakka ku ne mutanen nan, hikima za tă mutu tare da ku!
Sin duda ustedes son el pueblo, y la sabiduría terminará con ustedes.
3 Amma ni ma ina da hankali kamar ku; ba ku fi ni ba. Wane ne bai san duk waɗannan abubuwan ba?
Pero tengo una mente como ustedes; Soy igual a ustedes: sí, ¿quién no tiene conocimiento de cosas como estas?
4 “Na zama abin dariya ga abokaina, ko da yake na yi kira ga Allah ya kuwa amsa mini, duk da haka suka yi mini riya ko da yake ni mai adalci ne kuma marar laifi!
¡Parece que debo ser como uno que es motivo de burla a su prójimo, uno que hace su oración a Dios y recibe respuesta! ¡El hombre recto que no ha hecho nada malo es escarnecido!
5 Mutanen da ba su da damuwa suna jin daɗin ganin waɗanda suke dab da fāɗuwa.
En el pensamiento de aquel que está a gusto, no hay respeto por alguien que está en problemas; tal es el destino de aquellos cuyos pies se están deslizando.
6 Amma wurin zaman’yan fashi yana nan ba mai damunsu, waɗanda kuma suke saɓa wa Allah suna zamansu lafiya, har ma da masu ɗaukar allahnsu a hannuwansu.
Hay abundancia en las tiendas de aquellos que hacen la destrucción, y aquellos por quienes Dios es movido a la ira están a salvo; incluso aquellos los que Dios les ha dado el poder.
7 “Amma ka tambayi dabbobi, za su kuma koya maka, ko kuma tsuntsayen sararin sama kuma za su gaya maka.
Pero ahora pregunta a las bestias, y aprende de ellas; o a las aves del cielo, y te informarán;
8 Ko ka yi magana da duniya, za tă kuma koya maka, ko kuma ka bar kifin teku su sanar da kai.
O a las cosas en la tierra, y te darán sabiduría; Y los peces del mar te darán noticias de ello.
9 Wane ne cikin waɗannan bai san cewa hannun Ubangiji ne ya yi wannan ba?
¿Quién no ve por todos estos que la mano del Señor ha hecho esto?
10 Ran kowace halitta yana a hannunsa, haka kuma numfashin dukan’yan adam.
En cuya mano está el alma de todo ser viviente, y el aliento de toda carne humana.
11 Ko kunne ba ya gwada kalmomi kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci?
¿No son las palabras probadas por el oído, al igual que la comida se prueba por la boca?
12 Ko ba a wurin tsofaffi ake samun hikima ba? Ba tsawon rai yana kawo ganewa ba?
Los ancianos tienen sabiduría, y una larga vida da conocimiento.
13 “Allah ne mai iko da kuma hikima, shawara da ganewa nasa ne.
En Dios hay sabiduría y poder. El consejo y el conocimiento son suyos.
14 Abin da ya rushe ba a iya ginawa ba; in ya kulle mutum ba a iya buɗe shi a sake shi ba.
En verdad, no hay reconstrucción de lo que es derribado por Dios; cuando un hombre es aprisionado por Dios, nadie puede soltarlo.
15 Idan ya hana ruwan sama, za a yi fări; in kuma ya saki ruwa za a yi ambaliya.
En verdad, él retiene las aguas y están secas; Él los envía y la tierra se inunda.
16 Shi ne mai ƙarfi da kuma mai nasara; mai ruɗi da wanda aka ruɗa, duk nasa ne.
Con él están el poder y la sabiduría; el que es guiado al error, junto con su guía, está en sus manos;
17 Yakan sa mashawarta su zama marasa hikima yă kuma sa wawaye su zama masu shari’a.
Él quita la sabiduría de los guías sabios, y hace que los jueces sean necios;
18 Yana cire sarƙar da sarakuna suka ɗaura yă kuma ɗaura musu wata tsumma a kwankwaso.
Él deshace las cadenas de los reyes, y ata sus cinturas con lazos;
19 Yakan ƙasƙantar da firistoci yă kuma tumɓuke masu ikon da aka kafa tun da daɗewa.
Él hace a los sacerdotes prisioneros, volcando a los que están en posiciones seguras;
20 Yana sa amintattun mashawarta su yi shiru yakan kawar da hikimar dattawa.
Él hace las palabras de personas responsables sin efecto, y quita el entendimiento a los ancianos;
21 Yakan sa masu iko su ji kunya yă kuma ƙwace ƙarfin masu ƙarfi.
Él avergüenza a los jefes, y quita el poder de los fuertes;
22 Yana buɗe abubuwan da suke cikin duhu yă kuma kawo haske a wuraren da ba haske;
Descubriendo cosas profundas de la oscuridad, y saca la sombra profunda a la luz;
23 yana sa al’ummai su zama manya, sai kuma yă hallaka su; yana sa al’ummai su ƙasaita, yă kuma watsar da su.
Engrandece a las naciones y las destruye; Extendiendo las tierras de los pueblos, y luego las reúne.
24 Yana hana shugabannin duniya ganewa; Ya bar su su yi ta makuwa, su ruɗe, su ɓata.
Él quita la sabiduría de los gobernantes de la tierra, y los envía vagando en un desierto donde no hay camino.
25 Suna lallube cikin duhu ba haske; yă sa su yi ta tangaɗi kamar bugaggu.
Ellos van a tientas en la oscuridad sin luz, tambaleándose, como los borrachos.

< Ayuba 12 >