< Ayuba 12 >
2 “Ba shakka ku ne mutanen nan, hikima za tă mutu tare da ku!
Ciertamente que vosotros sois el pueblo; y con vosotros morirá la sabiduría.
3 Amma ni ma ina da hankali kamar ku; ba ku fi ni ba. Wane ne bai san duk waɗannan abubuwan ba?
También tengo yo seso como vosotros; no soy yo menos que vosotros: ¿y quién habrá que no pueda decir otro tanto?
4 “Na zama abin dariya ga abokaina, ko da yake na yi kira ga Allah ya kuwa amsa mini, duk da haka suka yi mini riya ko da yake ni mai adalci ne kuma marar laifi!
Yo soy uno de quien su amigo se mofa, que invoca á Dios, y él le responde: con todo, el justo y perfecto es escarnecido.
5 Mutanen da ba su da damuwa suna jin daɗin ganin waɗanda suke dab da fāɗuwa.
Aquel cuyos pies van á resbalar, [es como] una lámpara despreciada de aquel que está á sus anchuras.
6 Amma wurin zaman’yan fashi yana nan ba mai damunsu, waɗanda kuma suke saɓa wa Allah suna zamansu lafiya, har ma da masu ɗaukar allahnsu a hannuwansu.
Prosperan las tiendas de los ladrones, y los que provocan á Dios viven seguros; en cuyas manos él ha puesto [cuanto tienen].
7 “Amma ka tambayi dabbobi, za su kuma koya maka, ko kuma tsuntsayen sararin sama kuma za su gaya maka.
Y en efecto, pregunta ahora á las bestias, que ellas te enseñarán; y á las aves de los cielos, que ellas te lo mostrarán:
8 Ko ka yi magana da duniya, za tă kuma koya maka, ko kuma ka bar kifin teku su sanar da kai.
O habla á la tierra, que ella te enseñará; los peces de la mar te [lo] declararán también.
9 Wane ne cikin waɗannan bai san cewa hannun Ubangiji ne ya yi wannan ba?
¿Qué cosa de todas estas no entiende que la mano de Jehová la hizo?
10 Ran kowace halitta yana a hannunsa, haka kuma numfashin dukan’yan adam.
En su mano está el alma de todo viviente, y el espíritu de toda carne humana.
11 Ko kunne ba ya gwada kalmomi kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci?
Ciertamente el oído distingue las palabras, y el paladar gusta las viandas.
12 Ko ba a wurin tsofaffi ake samun hikima ba? Ba tsawon rai yana kawo ganewa ba?
En los viejos está la ciencia, y en la larga edad la inteligencia.
13 “Allah ne mai iko da kuma hikima, shawara da ganewa nasa ne.
Con Dios está la sabiduría y la fortaleza; suyo es el consejo y la inteligencia.
14 Abin da ya rushe ba a iya ginawa ba; in ya kulle mutum ba a iya buɗe shi a sake shi ba.
He aquí, él derribará, y no será edificado: encerrará al hombre, y no habrá quien le abra.
15 Idan ya hana ruwan sama, za a yi fări; in kuma ya saki ruwa za a yi ambaliya.
He aquí, él detendrá las aguas, y se secarán; él las enviará, y destruirán la tierra.
16 Shi ne mai ƙarfi da kuma mai nasara; mai ruɗi da wanda aka ruɗa, duk nasa ne.
Con él está la fortaleza y la existencia; suyo es el que yerra, y el que hace errar.
17 Yakan sa mashawarta su zama marasa hikima yă kuma sa wawaye su zama masu shari’a.
El hace andar á los consejeros desnudos [de consejo], y hace enloquecer á los jueces.
18 Yana cire sarƙar da sarakuna suka ɗaura yă kuma ɗaura musu wata tsumma a kwankwaso.
El suelta la atadura de los tiranos, y ata el cinto á sus lomos.
19 Yakan ƙasƙantar da firistoci yă kuma tumɓuke masu ikon da aka kafa tun da daɗewa.
El lleva despojados á los príncipes, y trastorna á los poderosos.
20 Yana sa amintattun mashawarta su yi shiru yakan kawar da hikimar dattawa.
El impide el labio á los que dicen verdad, y quita á los ancianos el consejo.
21 Yakan sa masu iko su ji kunya yă kuma ƙwace ƙarfin masu ƙarfi.
El derrama menosprecio sobre los príncipes, y enflaquece la fuerza de los esforzados.
22 Yana buɗe abubuwan da suke cikin duhu yă kuma kawo haske a wuraren da ba haske;
El descubre las profundidades de las tinieblas, y saca á luz la sombra de muerte.
23 yana sa al’ummai su zama manya, sai kuma yă hallaka su; yana sa al’ummai su ƙasaita, yă kuma watsar da su.
El multiplica las gentes, y él las destruye: él esparce las gentes, y las torna á recoger.
24 Yana hana shugabannin duniya ganewa; Ya bar su su yi ta makuwa, su ruɗe, su ɓata.
El quita el seso de las cabezas del pueblo de la tierra, y háceles que se pierdan vagueando sin camino:
25 Suna lallube cikin duhu ba haske; yă sa su yi ta tangaɗi kamar bugaggu.
Van á tientas como en tinieblas y sin luz, y los hace errar como borrachos.