< Ayuba 12 >
2 “Ba shakka ku ne mutanen nan, hikima za tă mutu tare da ku!
Entonces ciertamente ustedes son el pueblo, y con ustedes se acaba la sabiduría.
3 Amma ni ma ina da hankali kamar ku; ba ku fi ni ba. Wane ne bai san duk waɗannan abubuwan ba?
Pero yo tengo entendimiento como ustedes. No soy menos que ustedes. ¿Quién no sabe tales cosas?
4 “Na zama abin dariya ga abokaina, ko da yake na yi kira ga Allah ya kuwa amsa mini, duk da haka suka yi mini riya ko da yake ni mai adalci ne kuma marar laifi!
Yo soy alguien que para su amigo es motivo de risa, uno que clamó a ʼElohim y le respondió. ¡El justo e intachable es un payaso!
5 Mutanen da ba su da damuwa suna jin daɗin ganin waɗanda suke dab da fāɗuwa.
El que tiene bienestar desprecia la calamidad como algo preparado para aquellos que resbalan.
6 Amma wurin zaman’yan fashi yana nan ba mai damunsu, waɗanda kuma suke saɓa wa Allah suna zamansu lafiya, har ma da masu ɗaukar allahnsu a hannuwansu.
Prosperan las tiendas de los ladrones y los que provocan a ʼEL están seguros, aquellos que ʼEloah trae a su poder.
7 “Amma ka tambayi dabbobi, za su kuma koya maka, ko kuma tsuntsayen sararin sama kuma za su gaya maka.
En efecto, pregunta ahora a las bestias, y ellas te enseñarán, a las aves del cielo, y ellas te lo dirán.
8 Ko ka yi magana da duniya, za tă kuma koya maka, ko kuma ka bar kifin teku su sanar da kai.
O habla a la tierra, y te enseñará. Los peces del mar también te lo declararán.
9 Wane ne cikin waɗannan bai san cewa hannun Ubangiji ne ya yi wannan ba?
¿Cuál de ellos no sabe que la mano de Yavé hizo esto,
10 Ran kowace halitta yana a hannunsa, haka kuma numfashin dukan’yan adam.
que en su mano está la vida de todo viviente y el hálito de toda la humanidad?
11 Ko kunne ba ya gwada kalmomi kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci?
¿No distingue el oído las palabras y el paladar prueba la comida?
12 Ko ba a wurin tsofaffi ake samun hikima ba? Ba tsawon rai yana kawo ganewa ba?
En los ancianos está la sabiduría y en la larga edad el entendimiento.
13 “Allah ne mai iko da kuma hikima, shawara da ganewa nasa ne.
Con Él están la sabiduría y el poder. Suyos son el consejo y el entendimiento.
14 Abin da ya rushe ba a iya ginawa ba; in ya kulle mutum ba a iya buɗe shi a sake shi ba.
Si Él derriba, no será reedificado. Si Él encierra al hombre, no hay liberación.
15 Idan ya hana ruwan sama, za a yi fări; in kuma ya saki ruwa za a yi ambaliya.
Si Él retiene las aguas, se secan, y si las suelta, inundan la tierra.
16 Shi ne mai ƙarfi da kuma mai nasara; mai ruɗi da wanda aka ruɗa, duk nasa ne.
Con Él están la fortaleza y la sana sabiduría. Suyos son el que yerra y el que hace errar.
17 Yakan sa mashawarta su zama marasa hikima yă kuma sa wawaye su zama masu shari’a.
Hace andar descalzos a los consejeros y entontece a los jueces.
18 Yana cire sarƙar da sarakuna suka ɗaura yă kuma ɗaura musu wata tsumma a kwankwaso.
Suelta las ataduras que imponen los reyes y ata con una cuerda sus cinturas.
19 Yakan ƙasƙantar da firistoci yă kuma tumɓuke masu ikon da aka kafa tun da daɗewa.
Hace ir descalzos a los sacerdotes y derriba a los poderosos.
20 Yana sa amintattun mashawarta su yi shiru yakan kawar da hikimar dattawa.
Priva del habla a los de confianza, y del discernimiento a los ancianos.
21 Yakan sa masu iko su ji kunya yă kuma ƙwace ƙarfin masu ƙarfi.
Derrama desprecio sobre los nobles y afloja el cinturón de los fuertes.
22 Yana buɗe abubuwan da suke cikin duhu yă kuma kawo haske a wuraren da ba haske;
Descubre las profundidades de la oscuridad y saca a la luz la sombra de muerte.
23 yana sa al’ummai su zama manya, sai kuma yă hallaka su; yana sa al’ummai su ƙasaita, yă kuma watsar da su.
Engrandece las naciones y las destruye. Ensancha los pueblos y los suprime.
24 Yana hana shugabannin duniya ganewa; Ya bar su su yi ta makuwa, su ruɗe, su ɓata.
Priva de discreción a los caudillos de los pueblos de la tierra y los hace deambular por un desierto sin camino.
25 Suna lallube cikin duhu ba haske; yă sa su yi ta tangaɗi kamar bugaggu.
No tienen luz. Palpan en la oscuridad, y los hace tambalearse como ebrios.