< Ayuba 12 >
2 “Ba shakka ku ne mutanen nan, hikima za tă mutu tare da ku!
“De veras, vosotros sois hombres, y con vosotros morirá la sabiduría.
3 Amma ni ma ina da hankali kamar ku; ba ku fi ni ba. Wane ne bai san duk waɗannan abubuwan ba?
También yo tengo seso como vosotros; ninguna ventaja tenéis sobre mí; ¿y quién no sabe lo que decís?
4 “Na zama abin dariya ga abokaina, ko da yake na yi kira ga Allah ya kuwa amsa mini, duk da haka suka yi mini riya ko da yake ni mai adalci ne kuma marar laifi!
¡Ludibrio soy de mis amigos! ¡Yo, que clamaba a Dios, y Él le respondía! ¡Yo, el recto e inocente, ahora objeto de oprobio!
5 Mutanen da ba su da damuwa suna jin daɗin ganin waɗanda suke dab da fāɗuwa.
¡Ignominia al que sufre! —así piensa el que vive sin cuidados—. ¡Caiga desprecio sobre aquel cuyo pie resbala!
6 Amma wurin zaman’yan fashi yana nan ba mai damunsu, waɗanda kuma suke saɓa wa Allah suna zamansu lafiya, har ma da masu ɗaukar allahnsu a hannuwansu.
Las guaridas de los salteadores gozan de paz, seguros están los que irritan a Dios; a ellos Dios se lo otorga (todo).
7 “Amma ka tambayi dabbobi, za su kuma koya maka, ko kuma tsuntsayen sararin sama kuma za su gaya maka.
Pregunta, te ruego, a las bestias, y ellas te enseñarán, a las aves del cielo, y te lo dirán;
8 Ko ka yi magana da duniya, za tă kuma koya maka, ko kuma ka bar kifin teku su sanar da kai.
o habla con la tierra, y ella te instruirá; te lo contarán los peces del mar.
9 Wane ne cikin waɗannan bai san cewa hannun Ubangiji ne ya yi wannan ba?
¿Quién de todos estos seres no sabe que la mano de Yahvé ha hecho (todas) las cosas?
10 Ran kowace halitta yana a hannunsa, haka kuma numfashin dukan’yan adam.
En su mano está el alma de todo viviente, y el soplo de toda carne humana.
11 Ko kunne ba ya gwada kalmomi kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci?
¿No se ha hecho el oído para discernir las palabras; el paladar para gustar los manjares?
12 Ko ba a wurin tsofaffi ake samun hikima ba? Ba tsawon rai yana kawo ganewa ba?
En los ancianos reside la sabiduría, y en la larga vida la prudencia;
13 “Allah ne mai iko da kuma hikima, shawara da ganewa nasa ne.
con Él, empero, están la sabiduría y el poder, suyo es el consejo y suya la inteligencia.
14 Abin da ya rushe ba a iya ginawa ba; in ya kulle mutum ba a iya buɗe shi a sake shi ba.
Lo que Él derriba, no será reedificado; si Él encierra al hombre, no hay quien lo libre.
15 Idan ya hana ruwan sama, za a yi fări; in kuma ya saki ruwa za a yi ambaliya.
Si detiene las aguas, estas se secan; si las suelta, devastan la tierra.
16 Shi ne mai ƙarfi da kuma mai nasara; mai ruɗi da wanda aka ruɗa, duk nasa ne.
En Él están el poder y el saber, suyos son el engañado y el que engaña.
17 Yakan sa mashawarta su zama marasa hikima yă kuma sa wawaye su zama masu shari’a.
Él hace andar a los consejeros privados (de consejo), y entontece a los jueces.
18 Yana cire sarƙar da sarakuna suka ɗaura yă kuma ɗaura musu wata tsumma a kwankwaso.
Él quita a los reyes la faja, y les ciñe los lomos, con una soga.
19 Yakan ƙasƙantar da firistoci yă kuma tumɓuke masu ikon da aka kafa tun da daɗewa.
Hace andar a los sacerdotes descalzos, y a los grandes derriba.
20 Yana sa amintattun mashawarta su yi shiru yakan kawar da hikimar dattawa.
Quita el habla a los más respetados, y a los ancianos los priva del juicio.
21 Yakan sa masu iko su ji kunya yă kuma ƙwace ƙarfin masu ƙarfi.
Vacía desprecio sobre los príncipes, y afloja el cinto de los fuertes.
22 Yana buɗe abubuwan da suke cikin duhu yă kuma kawo haske a wuraren da ba haske;
Descubre lo oculto en las tinieblas, y saca a luz la sombra de la muerte.
23 yana sa al’ummai su zama manya, sai kuma yă hallaka su; yana sa al’ummai su ƙasaita, yă kuma watsar da su.
Da prosperidad a los pueblos y los destruye, dilata a las naciones, y las reduce.
24 Yana hana shugabannin duniya ganewa; Ya bar su su yi ta makuwa, su ruɗe, su ɓata.
Quita la inteligencia a los príncipes de los pueblos de la tierra, y los hace vagar por un desierto sin camino;
25 Suna lallube cikin duhu ba haske; yă sa su yi ta tangaɗi kamar bugaggu.
andan a tientas en tinieblas, sin tener luz; Él los hace errar como a embriagados.”