< Ayuba 12 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Potem Hiob odpowiedział:
2 “Ba shakka ku ne mutanen nan, hikima za tă mutu tare da ku!
Doprawdy jesteście ludem i wraz z wami zginie mądrość.
3 Amma ni ma ina da hankali kamar ku; ba ku fi ni ba. Wane ne bai san duk waɗannan abubuwan ba?
Ale ja również mam rozum, jak [i] wy, i nie jestem od was gorszy. Kto nie zna tych rzeczy?
4 “Na zama abin dariya ga abokaina, ko da yake na yi kira ga Allah ya kuwa amsa mini, duk da haka suka yi mini riya ko da yake ni mai adalci ne kuma marar laifi!
Jestem pośmiewiskiem dla swojego przyjaciela; ja, który wołam do Boga, a on odpowiada; sprawiedliwy [i] doskonały [jest] pośmiewiskiem.
5 Mutanen da ba su da damuwa suna jin daɗin ganin waɗanda suke dab da fāɗuwa.
Ten, który jest bliski upadku, to pochodnia wzgardzona w umyśle [tego], który żyje w pokoju.
6 Amma wurin zaman’yan fashi yana nan ba mai damunsu, waɗanda kuma suke saɓa wa Allah suna zamansu lafiya, har ma da masu ɗaukar allahnsu a hannuwansu.
Namioty łupieżców są spokojne i bezpieczni są ci, którzy drażnią Boga, a którym Bóg [obficie] daje w ręce.
7 “Amma ka tambayi dabbobi, za su kuma koya maka, ko kuma tsuntsayen sararin sama kuma za su gaya maka.
Ale zapytaj zwierząt, a one cię pouczą, i ptaków nieba, a powiedzą tobie.
8 Ko ka yi magana da duniya, za tă kuma koya maka, ko kuma ka bar kifin teku su sanar da kai.
Albo rozmawiaj z ziemią, a ona cię nauczy, i opowiedzą ci ryby morskie.
9 Wane ne cikin waɗannan bai san cewa hannun Ubangiji ne ya yi wannan ba?
Któż spośród nich wszystkich nie wie, że ręka PANA to wykonała?
10 Ran kowace halitta yana a hannunsa, haka kuma numfashin dukan’yan adam.
W jego ręku jest dusza wszelkiej istoty żywej i duch wszelkiego człowieka.
11 Ko kunne ba ya gwada kalmomi kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci?
Czy ucho nie bada mowy, a podniebienie nie smakuje pokarmu?
12 Ko ba a wurin tsofaffi ake samun hikima ba? Ba tsawon rai yana kawo ganewa ba?
U starców jest mądrość, a w długości dni roztropność.
13 “Allah ne mai iko da kuma hikima, shawara da ganewa nasa ne.
[Ale] u niego jest mądrość i siła, u niego rada i roztropność.
14 Abin da ya rushe ba a iya ginawa ba; in ya kulle mutum ba a iya buɗe shi a sake shi ba.
Oto on burzy, [a] nikt nie może odbudować, zamyka człowieka, a nikt nie może otworzyć.
15 Idan ya hana ruwan sama, za a yi fări; in kuma ya saki ruwa za a yi ambaliya.
Oto gdy zatrzyma wody, wysychają, gdy je wypuści, wywracają ziemię.
16 Shi ne mai ƙarfi da kuma mai nasara; mai ruɗi da wanda aka ruɗa, duk nasa ne.
U niego jest moc i mądrość. Do niego należy zwiedziony i zwodziciel.
17 Yakan sa mashawarta su zama marasa hikima yă kuma sa wawaye su zama masu shari’a.
Pozbawia radców [mądrości] i sędziów czyni głupcami.
18 Yana cire sarƙar da sarakuna suka ɗaura yă kuma ɗaura musu wata tsumma a kwankwaso.
Rozwiązuje więzy królów i przepasuje ich biodra pasem.
19 Yakan ƙasƙantar da firistoci yă kuma tumɓuke masu ikon da aka kafa tun da daɗewa.
Odprowadza złupionych książąt i wywraca mocarzy.
20 Yana sa amintattun mashawarta su yi shiru yakan kawar da hikimar dattawa.
Odbiera mowę prawdomównym i zabiera starcom rozsądek.
21 Yakan sa masu iko su ji kunya yă kuma ƙwace ƙarfin masu ƙarfi.
Wylewa pogardę na książąt i osłabia siły mocarzy.
22 Yana buɗe abubuwan da suke cikin duhu yă kuma kawo haske a wuraren da ba haske;
[On] odsłania głębokie rzeczy z ciemności i wyprowadza na światło cień śmierci.
23 yana sa al’ummai su zama manya, sai kuma yă hallaka su; yana sa al’ummai su ƙasaita, yă kuma watsar da su.
Rozmnaża narody i wytraca je, rozszerza narody i pomniejsza je.
24 Yana hana shugabannin duniya ganewa; Ya bar su su yi ta makuwa, su ruɗe, su ɓata.
On zabiera serca przełożonym ludu ziemi i sprawia, że błądzą po pustyni bezdrożnej;
25 Suna lallube cikin duhu ba haske; yă sa su yi ta tangaɗi kamar bugaggu.
I chodzą po omacku w ciemności bez światła, i sprawia, że zataczają się jak pijani.

< Ayuba 12 >