< Ayuba 12 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Respondens autem Iob, dixit:
2 “Ba shakka ku ne mutanen nan, hikima za tă mutu tare da ku!
Ergo vos estis soli homines, et vobiscum morietur sapientia?
3 Amma ni ma ina da hankali kamar ku; ba ku fi ni ba. Wane ne bai san duk waɗannan abubuwan ba?
Et mihi est cor sicut et vobis, nec inferior vestri sum: quis enim hæc, quæ nostis, ignorat?
4 “Na zama abin dariya ga abokaina, ko da yake na yi kira ga Allah ya kuwa amsa mini, duk da haka suka yi mini riya ko da yake ni mai adalci ne kuma marar laifi!
Qui deridetur ab amico suo sicut ego, invocabit Deum, et exaudiet eum: deridetur enim iusti simplicitas.
5 Mutanen da ba su da damuwa suna jin daɗin ganin waɗanda suke dab da fāɗuwa.
Lampas contempta apud cogitationes divitum, parata ad tempus statutum.
6 Amma wurin zaman’yan fashi yana nan ba mai damunsu, waɗanda kuma suke saɓa wa Allah suna zamansu lafiya, har ma da masu ɗaukar allahnsu a hannuwansu.
Abundant tabernacula prædonum, et audacter provocant Deum, cum ipse dederit omnia in manus eorum.
7 “Amma ka tambayi dabbobi, za su kuma koya maka, ko kuma tsuntsayen sararin sama kuma za su gaya maka.
Nimirum interroga iumenta, et docebunt te: et volatilia cæli, et indicabunt tibi.
8 Ko ka yi magana da duniya, za tă kuma koya maka, ko kuma ka bar kifin teku su sanar da kai.
Loquere terræ, et respondebit tibi: et narrabunt pisces maris.
9 Wane ne cikin waɗannan bai san cewa hannun Ubangiji ne ya yi wannan ba?
Quis ignorat quod omnia hæc manus Domini fecerit?
10 Ran kowace halitta yana a hannunsa, haka kuma numfashin dukan’yan adam.
In cuius manu anima omnis viventis, et spiritus universæ carnis hominis.
11 Ko kunne ba ya gwada kalmomi kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci?
Nonne auris verba diiudicat, et fauces comedentis, saporem?
12 Ko ba a wurin tsofaffi ake samun hikima ba? Ba tsawon rai yana kawo ganewa ba?
In antiquis est sapientia, et in multo tempore prudentia.
13 “Allah ne mai iko da kuma hikima, shawara da ganewa nasa ne.
Apud ipsum est sapientia et fortitudo, ipse habet consilium et intelligentiam.
14 Abin da ya rushe ba a iya ginawa ba; in ya kulle mutum ba a iya buɗe shi a sake shi ba.
Si destruxerit, nemo est qui ædificet: si incluserit hominem, nullus est qui aperiat.
15 Idan ya hana ruwan sama, za a yi fări; in kuma ya saki ruwa za a yi ambaliya.
Si continuerit aquas, omnia siccabuntur: et si emiserit eas, subvertent terram.
16 Shi ne mai ƙarfi da kuma mai nasara; mai ruɗi da wanda aka ruɗa, duk nasa ne.
Apud ipsum est fortitudo et sapientia: ipse novit et decipientem, et eum qui decipitur.
17 Yakan sa mashawarta su zama marasa hikima yă kuma sa wawaye su zama masu shari’a.
Adducit consiliarios in stultum finem, et iudices in stuporem.
18 Yana cire sarƙar da sarakuna suka ɗaura yă kuma ɗaura musu wata tsumma a kwankwaso.
Balteum regum dissolvit, et præcingit fune renes eorum.
19 Yakan ƙasƙantar da firistoci yă kuma tumɓuke masu ikon da aka kafa tun da daɗewa.
Ducit sacerdotes inglorios, et optimates supplantat:
20 Yana sa amintattun mashawarta su yi shiru yakan kawar da hikimar dattawa.
Commutans labium veracium, et doctrinam senum auferens.
21 Yakan sa masu iko su ji kunya yă kuma ƙwace ƙarfin masu ƙarfi.
Effundit despectionem super principes, eos, qui oppressi fuerant, relevans.
22 Yana buɗe abubuwan da suke cikin duhu yă kuma kawo haske a wuraren da ba haske;
Qui revelat profunda de tenebris, et producit in lucem umbram mortis.
23 yana sa al’ummai su zama manya, sai kuma yă hallaka su; yana sa al’ummai su ƙasaita, yă kuma watsar da su.
Qui multiplicat gentes et perdit eas, et subversas in integrum restituit.
24 Yana hana shugabannin duniya ganewa; Ya bar su su yi ta makuwa, su ruɗe, su ɓata.
Qui immutat cor principum populi terræ, et decipit eos ut frustra incedant per invium:
25 Suna lallube cikin duhu ba haske; yă sa su yi ta tangaɗi kamar bugaggu.
Palpabunt quasi in tenebris, et non in luce, et errare eos faciet quasi ebrios.

< Ayuba 12 >