< Ayuba 12 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Mais Job répondit, et dit:
2 “Ba shakka ku ne mutanen nan, hikima za tă mutu tare da ku!
Vraiment, êtes-vous tout un peuple; et la sagesse mourra-t-elle avec vous?
3 Amma ni ma ina da hankali kamar ku; ba ku fi ni ba. Wane ne bai san duk waɗannan abubuwan ba?
J'ai du bon sens aussi bien que vous, et je ne vous suis point inférieur; et qui [est-ce qui ne sait] de telles choses?
4 “Na zama abin dariya ga abokaina, ko da yake na yi kira ga Allah ya kuwa amsa mini, duk da haka suka yi mini riya ko da yake ni mai adalci ne kuma marar laifi!
Je suis un homme qui est en risée à son ami, [mais] qui invoquera Dieu, et Dieu lui répondra. On se moque d'un homme qui est juste et droit.
5 Mutanen da ba su da damuwa suna jin daɗin ganin waɗanda suke dab da fāɗuwa.
Celui dont les pieds sont tout prêts à glisser, est selon la pensée de celui qui est à son aise, un flambeau dont on ne tient plus de compte.
6 Amma wurin zaman’yan fashi yana nan ba mai damunsu, waɗanda kuma suke saɓa wa Allah suna zamansu lafiya, har ma da masu ɗaukar allahnsu a hannuwansu.
Ce sont les tentes des voleurs [qui] prospèrent, et ceux-là sont assurés qui irritent le [Dieu] Fort, et ils sont ceux à qui Dieu remet tout entre les mains.
7 “Amma ka tambayi dabbobi, za su kuma koya maka, ko kuma tsuntsayen sararin sama kuma za su gaya maka.
Et, en effet, je te prie, interroge les bêtes, et [chacune d'elles] t'enseignera; ou les oiseaux des cieux, et ils te le déclareront;
8 Ko ka yi magana da duniya, za tă kuma koya maka, ko kuma ka bar kifin teku su sanar da kai.
Ou parle à la terre, et elle t'enseignera; même les poissons de la mer te le raconteront;
9 Wane ne cikin waɗannan bai san cewa hannun Ubangiji ne ya yi wannan ba?
Qui est-ce qui ne sait toutes ces choses, [et] que c'est la main de l'Eternel qui a fait cela?
10 Ran kowace halitta yana a hannunsa, haka kuma numfashin dukan’yan adam.
[Car c'est lui] en la main duquel est l'âme de tout ce qui vit, et l'esprit de toute chair humaine.
11 Ko kunne ba ya gwada kalmomi kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci?
L'oreille ne discerne-t-elle pas les discours, ainsi que le palais savoure les viandes?
12 Ko ba a wurin tsofaffi ake samun hikima ba? Ba tsawon rai yana kawo ganewa ba?
La sagesse est dans les vieillards, et l'intelligence [est le fruit] d'une longue vie.
13 “Allah ne mai iko da kuma hikima, shawara da ganewa nasa ne.
Mais en lui est la sagesse et la force; à lui appartient le conseil et l'intelligence.
14 Abin da ya rushe ba a iya ginawa ba; in ya kulle mutum ba a iya buɗe shi a sake shi ba.
Voilà, il démolira, et on ne rebâtira point; s'il ferme sur quelqu'un, on n'ouvrira point.
15 Idan ya hana ruwan sama, za a yi fări; in kuma ya saki ruwa za a yi ambaliya.
Voilà, il retiendra les eaux, et tout deviendra sec; il les lâchera, et elles renverseront la terre.
16 Shi ne mai ƙarfi da kuma mai nasara; mai ruɗi da wanda aka ruɗa, duk nasa ne.
En lui est la force et l'intelligence; à lui est celui qui s'égare, et celui qui le fait égarer.
17 Yakan sa mashawarta su zama marasa hikima yă kuma sa wawaye su zama masu shari’a.
Il emmène dépouillés les conseillers, et il met hors du sens les juges.
18 Yana cire sarƙar da sarakuna suka ɗaura yă kuma ɗaura musu wata tsumma a kwankwaso.
Il détache la ceinture des Rois, et il serre leurs reins de sangles.
19 Yakan ƙasƙantar da firistoci yă kuma tumɓuke masu ikon da aka kafa tun da daɗewa.
Il emmène nus ceux qui sont en autorité, et il renverse les forts.
20 Yana sa amintattun mashawarta su yi shiru yakan kawar da hikimar dattawa.
Il ôte la parole à ceux qui sont les plus assurés en leurs discours, et il prive de sens les anciens.
21 Yakan sa masu iko su ji kunya yă kuma ƙwace ƙarfin masu ƙarfi.
Il répand le mépris sur les principaux; il rend lâche la ceinture des forts.
22 Yana buɗe abubuwan da suke cikin duhu yă kuma kawo haske a wuraren da ba haske;
Il met en évidence les choses qui étaient cachées dans les ténèbres, et il produit en lumière l'ombre de la mort.
23 yana sa al’ummai su zama manya, sai kuma yă hallaka su; yana sa al’ummai su ƙasaita, yă kuma watsar da su.
Il multiplie les nations, et les fait périr; il répand çà et là les nations, et puis il les ramène.
24 Yana hana shugabannin duniya ganewa; Ya bar su su yi ta makuwa, su ruɗe, su ɓata.
Il ôte le cœur aux Chefs des peuples de la terre, et les fait errer dans les déserts où il n'y a point de chemin.
25 Suna lallube cikin duhu ba haske; yă sa su yi ta tangaɗi kamar bugaggu.
Ils vont à tâtons dans les ténèbres, sans aucune clarté, et il les fait chanceler comme des gens ivres.

< Ayuba 12 >