< Ayuba 12 >
And Job answereth and saith: —
2 “Ba shakka ku ne mutanen nan, hikima za tă mutu tare da ku!
Truly — ye [are] the people, And with you doth wisdom die.
3 Amma ni ma ina da hankali kamar ku; ba ku fi ni ba. Wane ne bai san duk waɗannan abubuwan ba?
I also have a heart like you, I am not fallen more than you, And with whom is there not like these?
4 “Na zama abin dariya ga abokaina, ko da yake na yi kira ga Allah ya kuwa amsa mini, duk da haka suka yi mini riya ko da yake ni mai adalci ne kuma marar laifi!
A laughter to his friend I am: 'He calleth to God, and He answereth him,' A laughter [is] the perfect righteous one.
5 Mutanen da ba su da damuwa suna jin daɗin ganin waɗanda suke dab da fāɗuwa.
A torch — despised in the thoughts of the secure Is prepared for those sliding with the feet.
6 Amma wurin zaman’yan fashi yana nan ba mai damunsu, waɗanda kuma suke saɓa wa Allah suna zamansu lafiya, har ma da masu ɗaukar allahnsu a hannuwansu.
At peace are the tents of spoilers, And those provoking God have confidence, He into whose hand God hath brought.
7 “Amma ka tambayi dabbobi, za su kuma koya maka, ko kuma tsuntsayen sararin sama kuma za su gaya maka.
And yet, ask, I pray thee, [One of] the beasts, and it doth shew thee, And a fowl of the heavens, And it doth declare to thee.
8 Ko ka yi magana da duniya, za tă kuma koya maka, ko kuma ka bar kifin teku su sanar da kai.
Or talk to the earth, and it sheweth thee, And fishes of the sea recount to thee:
9 Wane ne cikin waɗannan bai san cewa hannun Ubangiji ne ya yi wannan ba?
'Who hath not known in all these, That the hand of Jehovah hath done this?
10 Ran kowace halitta yana a hannunsa, haka kuma numfashin dukan’yan adam.
In whose hand [is] the breath of every living thing, And the spirit of all flesh of man.'
11 Ko kunne ba ya gwada kalmomi kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci?
Doth not the ear try words? And the palate taste food for itself?
12 Ko ba a wurin tsofaffi ake samun hikima ba? Ba tsawon rai yana kawo ganewa ba?
With the very aged [is] wisdom, And [with] length of days understanding.
13 “Allah ne mai iko da kuma hikima, shawara da ganewa nasa ne.
With Him [are] wisdom and might, To him [are] counsel and understanding.
14 Abin da ya rushe ba a iya ginawa ba; in ya kulle mutum ba a iya buɗe shi a sake shi ba.
Lo, He breaketh down, and it is not built up, He shutteth against a man, And it is not opened.
15 Idan ya hana ruwan sama, za a yi fări; in kuma ya saki ruwa za a yi ambaliya.
Lo, He keepeth in the waters, and they are dried up, And he sendeth them forth, And they overturn the land.
16 Shi ne mai ƙarfi da kuma mai nasara; mai ruɗi da wanda aka ruɗa, duk nasa ne.
With Him [are] strength and wisdom, His the deceived and deceiver.
17 Yakan sa mashawarta su zama marasa hikima yă kuma sa wawaye su zama masu shari’a.
Causing counsellors to go away a spoil, And judges He maketh foolish.
18 Yana cire sarƙar da sarakuna suka ɗaura yă kuma ɗaura musu wata tsumma a kwankwaso.
The bands of kings He hath opened, And He bindeth a girdle on their loins.
19 Yakan ƙasƙantar da firistoci yă kuma tumɓuke masu ikon da aka kafa tun da daɗewa.
Causing ministers to go away a spoil And strong ones He overthroweth.
20 Yana sa amintattun mashawarta su yi shiru yakan kawar da hikimar dattawa.
Turning aside the lip of the stedfast, And the reason of the aged He taketh away.
21 Yakan sa masu iko su ji kunya yă kuma ƙwace ƙarfin masu ƙarfi.
Pouring contempt upon princes, And the girdle of the mighty He made feeble.
22 Yana buɗe abubuwan da suke cikin duhu yă kuma kawo haske a wuraren da ba haske;
Removing deep things out of darkness, And He bringeth out to light death-shade.
23 yana sa al’ummai su zama manya, sai kuma yă hallaka su; yana sa al’ummai su ƙasaita, yă kuma watsar da su.
Magnifying the nations, and He destroyeth them, Spreading out the nations, and He quieteth them.
24 Yana hana shugabannin duniya ganewa; Ya bar su su yi ta makuwa, su ruɗe, su ɓata.
Turning aside the heart Of the heads of the people of the land, And he causeth them to wander In vacancy — no way!
25 Suna lallube cikin duhu ba haske; yă sa su yi ta tangaɗi kamar bugaggu.
They feel darkness, and not light, He causeth them to wander as a drunkard.