< Ayuba 12 >
Then Job answered and said:
2 “Ba shakka ku ne mutanen nan, hikima za tă mutu tare da ku!
No doubt ye are the whole people! And wisdom will die with you!
3 Amma ni ma ina da hankali kamar ku; ba ku fi ni ba. Wane ne bai san duk waɗannan abubuwan ba?
But I have understanding as well as you; I am not inferior to you: Yea, who knoweth not such things as these?
4 “Na zama abin dariya ga abokaina, ko da yake na yi kira ga Allah ya kuwa amsa mini, duk da haka suka yi mini riya ko da yake ni mai adalci ne kuma marar laifi!
I am become a laughing-stock to my friend, —I who call upon God, that he would answer me! The innocent and upright man is held in derision.
5 Mutanen da ba su da damuwa suna jin daɗin ganin waɗanda suke dab da fāɗuwa.
To calamity belongeth contempt in the mind of one at ease; It is ready for them that slip with the feet.
6 Amma wurin zaman’yan fashi yana nan ba mai damunsu, waɗanda kuma suke saɓa wa Allah suna zamansu lafiya, har ma da masu ɗaukar allahnsu a hannuwansu.
The tents of robbers are in prosperity, And they who provoke God are secure, Who carry their God in their hand.
7 “Amma ka tambayi dabbobi, za su kuma koya maka, ko kuma tsuntsayen sararin sama kuma za su gaya maka.
For ask now the beasts, and they will teach thee; Or the fowls of the air, and they will tell thee;
8 Ko ka yi magana da duniya, za tă kuma koya maka, ko kuma ka bar kifin teku su sanar da kai.
Or speak to the earth, and it will instruct thee; And the fishes of the sea will declare unto thee.
9 Wane ne cikin waɗannan bai san cewa hannun Ubangiji ne ya yi wannan ba?
Who among all these doth not know That the hand of Jehovah doeth these things?
10 Ran kowace halitta yana a hannunsa, haka kuma numfashin dukan’yan adam.
In whose hand is the soul of every living thing, And the breath of all mankind.
11 Ko kunne ba ya gwada kalmomi kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci?
Doth not the ear prove words, As the mouth tasteth meat?
12 Ko ba a wurin tsofaffi ake samun hikima ba? Ba tsawon rai yana kawo ganewa ba?
With the aged is wisdom, And with length of days is understanding.
13 “Allah ne mai iko da kuma hikima, shawara da ganewa nasa ne.
With Him are wisdom and strength; With Him counsel and understanding.
14 Abin da ya rushe ba a iya ginawa ba; in ya kulle mutum ba a iya buɗe shi a sake shi ba.
Lo! he pulleth down, and it shall not be rebuilt; He bindeth a man, and he shall not be set loose.
15 Idan ya hana ruwan sama, za a yi fări; in kuma ya saki ruwa za a yi ambaliya.
Lo! he withholdeth the waters, and they are dried up; He sendeth them forth, and they lay waste the earth.
16 Shi ne mai ƙarfi da kuma mai nasara; mai ruɗi da wanda aka ruɗa, duk nasa ne.
With him are strength and wisdom; The deceived and the deceiver are his.
17 Yakan sa mashawarta su zama marasa hikima yă kuma sa wawaye su zama masu shari’a.
He leadeth counsellors away captive, And judges he maketh fools.
18 Yana cire sarƙar da sarakuna suka ɗaura yă kuma ɗaura musu wata tsumma a kwankwaso.
He looseth the authority of kings, And bindeth their loins with a cord.
19 Yakan ƙasƙantar da firistoci yă kuma tumɓuke masu ikon da aka kafa tun da daɗewa.
He leadeth priests away captive, And overthroweth the mighty.
20 Yana sa amintattun mashawarta su yi shiru yakan kawar da hikimar dattawa.
He removeth speech from the trusty, And taketh away judgment from the elders.
21 Yakan sa masu iko su ji kunya yă kuma ƙwace ƙarfin masu ƙarfi.
He poureth contempt upon princes, And looseth the girdle of the mighty.
22 Yana buɗe abubuwan da suke cikin duhu yă kuma kawo haske a wuraren da ba haske;
He revealeth deep things out of darkness, And bringeth the shadow of death to light.
23 yana sa al’ummai su zama manya, sai kuma yă hallaka su; yana sa al’ummai su ƙasaita, yă kuma watsar da su.
He exalteth nations, and destroyeth them; He enlargeth nations, and leadeth them captive.
24 Yana hana shugabannin duniya ganewa; Ya bar su su yi ta makuwa, su ruɗe, su ɓata.
He taketh away the understanding of the great men of the land, And causeth them to wander in a wilderness, where is no path;
25 Suna lallube cikin duhu ba haske; yă sa su yi ta tangaɗi kamar bugaggu.
They grope in the dark without light; He maketh them stagger like a drunken man.