< Ayuba 12 >
Then answered Job, and said,
2 “Ba shakka ku ne mutanen nan, hikima za tă mutu tare da ku!
Truly ye are indeed the [right kind of] people, and with you wisdom must die out.
3 Amma ni ma ina da hankali kamar ku; ba ku fi ni ba. Wane ne bai san duk waɗannan abubuwan ba?
I also have sense like you; I do not fall short compared with you: and who possesseth not such things as these?
4 “Na zama abin dariya ga abokaina, ko da yake na yi kira ga Allah ya kuwa amsa mini, duk da haka suka yi mini riya ko da yake ni mai adalci ne kuma marar laifi!
I am as one laughed at by his friend, who calleth upon God, while he answered him: [yea, ] a laughing-stock though righteous and innocent.
5 Mutanen da ba su da damuwa suna jin daɗin ganin waɗanda suke dab da fāɗuwa.
To the unfortunate there is given contempt— according to the thoughts of him that is at ease— prepared [also] for those whose foot slippeth.
6 Amma wurin zaman’yan fashi yana nan ba mai damunsu, waɗanda kuma suke saɓa wa Allah suna zamansu lafiya, har ma da masu ɗaukar allahnsu a hannuwansu.
Prosperous are the tents of robbers, and security is given to those that provoke God. to him who carrieth his god in his hand.
7 “Amma ka tambayi dabbobi, za su kuma koya maka, ko kuma tsuntsayen sararin sama kuma za su gaya maka.
Yet, do only ask of the beasts, and they will instruct thee; and the fowls of the heavens, and they will tell it thee;
8 Ko ka yi magana da duniya, za tă kuma koya maka, ko kuma ka bar kifin teku su sanar da kai.
Or speak to the earth, and she will instruct thee; and the fishes of the sea will inform thee
9 Wane ne cikin waɗannan bai san cewa hannun Ubangiji ne ya yi wannan ba?
Who knoweth not through all these that the hand of the Lord hath wrought this?
10 Ran kowace halitta yana a hannunsa, haka kuma numfashin dukan’yan adam.
[He] in whose hand is the soul of every living thing, and the spirit of all the bodies of men?
11 Ko kunne ba ya gwada kalmomi kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci?
Doth not the ear try words, as the palate tasteth food for itself?
12 Ko ba a wurin tsofaffi ake samun hikima ba? Ba tsawon rai yana kawo ganewa ba?
So It with the ancients wisdom, and with [those of] length of days understanding,
13 “Allah ne mai iko da kuma hikima, shawara da ganewa nasa ne.
That with him are wisdom and strength, his are counsel and understanding.
14 Abin da ya rushe ba a iya ginawa ba; in ya kulle mutum ba a iya buɗe shi a sake shi ba.
Behold, he pulleth down, and there can be no rebuilding: he locketh [the prison] upon a man, and there can be no opening,
15 Idan ya hana ruwan sama, za a yi fări; in kuma ya saki ruwa za a yi ambaliya.
Behold, he restraineth the waters, and they dry up; or he suffereth them to flow, and they overturn the earth.
16 Shi ne mai ƙarfi da kuma mai nasara; mai ruɗi da wanda aka ruɗa, duk nasa ne.
With him are strength and counsel: his are the deceived and the deceiver.
17 Yakan sa mashawarta su zama marasa hikima yă kuma sa wawaye su zama masu shari’a.
He leadeth counsellors away bereft of sense, and maketh the judges fools.
18 Yana cire sarƙar da sarakuna suka ɗaura yă kuma ɗaura musu wata tsumma a kwankwaso.
He looseth the bond of kings, and bindeth a girdle around their loins.
19 Yakan ƙasƙantar da firistoci yă kuma tumɓuke masu ikon da aka kafa tun da daɗewa.
He leadeth priests away bereft of sense, and the powerful he causeth to walk on crooked paths.
20 Yana sa amintattun mashawarta su yi shiru yakan kawar da hikimar dattawa.
He removeth the speech from trusty speakers, and taketh away the intelligence of the aged.
21 Yakan sa masu iko su ji kunya yă kuma ƙwace ƙarfin masu ƙarfi.
He poureth contempt upon princes, and the belt of the mighty be looseneth.
22 Yana buɗe abubuwan da suke cikin duhu yă kuma kawo haske a wuraren da ba haske;
He layeth open deep things from the midst of darkness, and bringeth out unto light the shadow of death.
23 yana sa al’ummai su zama manya, sai kuma yă hallaka su; yana sa al’ummai su ƙasaita, yă kuma watsar da su.
He permitteth the nations to become great, and destroyeth them: he spreadeth out the nations, and leadeth them away.
24 Yana hana shugabannin duniya ganewa; Ya bar su su yi ta makuwa, su ruɗe, su ɓata.
He taketh away the sense of the chiefs of the people of the land, and causeth them to wander astray in a wilderness when there is no way.
25 Suna lallube cikin duhu ba haske; yă sa su yi ta tangaɗi kamar bugaggu.
They grope in the dark without light, and he causeth them to wander astray like a drunken man.