< Ayuba 12 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
And Job answered and said,
2 “Ba shakka ku ne mutanen nan, hikima za tă mutu tare da ku!
Truly ye are the people, and wisdom shall die with you!
3 Amma ni ma ina da hankali kamar ku; ba ku fi ni ba. Wane ne bai san duk waɗannan abubuwan ba?
I also have understanding as well as you; I am not inferior to you; and who knoweth not such things as these?
4 “Na zama abin dariya ga abokaina, ko da yake na yi kira ga Allah ya kuwa amsa mini, duk da haka suka yi mini riya ko da yake ni mai adalci ne kuma marar laifi!
I am to be one that is a derision to his friend, I who call upon God, and whom he will answer: a derision is the just upright [man].
5 Mutanen da ba su da damuwa suna jin daɗin ganin waɗanda suke dab da fāɗuwa.
He that is ready to stumble with the foot is a lamp despised in the thought of him that is at ease.
6 Amma wurin zaman’yan fashi yana nan ba mai damunsu, waɗanda kuma suke saɓa wa Allah suna zamansu lafiya, har ma da masu ɗaukar allahnsu a hannuwansu.
The tents of desolators are in peace, and they that provoke God are secure; into whose hand God bringeth.
7 “Amma ka tambayi dabbobi, za su kuma koya maka, ko kuma tsuntsayen sararin sama kuma za su gaya maka.
But ask now the beasts, and they shall teach thee; and the fowl of the heavens, and they shall tell thee;
8 Ko ka yi magana da duniya, za tă kuma koya maka, ko kuma ka bar kifin teku su sanar da kai.
Or speak to the earth, and it shall teach thee; and the fishes of the sea shall declare unto thee.
9 Wane ne cikin waɗannan bai san cewa hannun Ubangiji ne ya yi wannan ba?
Who knoweth not in all these, that the hand of Jehovah hath wrought this?
10 Ran kowace halitta yana a hannunsa, haka kuma numfashin dukan’yan adam.
In whose hand is the soul of every living thing, and the spirit of all flesh of man.
11 Ko kunne ba ya gwada kalmomi kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci?
Doth not the ear try words, as the palate tasteth food?
12 Ko ba a wurin tsofaffi ake samun hikima ba? Ba tsawon rai yana kawo ganewa ba?
With the aged is wisdom, and in length of days understanding.
13 “Allah ne mai iko da kuma hikima, shawara da ganewa nasa ne.
With him is wisdom and might; he hath counsel and understanding.
14 Abin da ya rushe ba a iya ginawa ba; in ya kulle mutum ba a iya buɗe shi a sake shi ba.
Behold, he breaketh down, and it is not built again; he shutteth up a man, and there is no opening.
15 Idan ya hana ruwan sama, za a yi fări; in kuma ya saki ruwa za a yi ambaliya.
Behold, he withholdeth the waters, and they dry up; and he sendeth them out, and they overturn the earth.
16 Shi ne mai ƙarfi da kuma mai nasara; mai ruɗi da wanda aka ruɗa, duk nasa ne.
With him is strength and effectual knowledge; the deceived and the deceiver are his.
17 Yakan sa mashawarta su zama marasa hikima yă kuma sa wawaye su zama masu shari’a.
He leadeth counsellors away spoiled, and judges maketh he fools;
18 Yana cire sarƙar da sarakuna suka ɗaura yă kuma ɗaura musu wata tsumma a kwankwaso.
He weakeneth the government of kings, and bindeth their loins with a fetter;
19 Yakan ƙasƙantar da firistoci yă kuma tumɓuke masu ikon da aka kafa tun da daɗewa.
He leadeth priests away spoiled, and overthroweth the mighty;
20 Yana sa amintattun mashawarta su yi shiru yakan kawar da hikimar dattawa.
He depriveth of speech the trusty, and taketh away the judgment of the elders;
21 Yakan sa masu iko su ji kunya yă kuma ƙwace ƙarfin masu ƙarfi.
He poureth contempt upon nobles, and slackeneth the girdle of the mighty;
22 Yana buɗe abubuwan da suke cikin duhu yă kuma kawo haske a wuraren da ba haske;
He discovereth deep things out of darkness, and bringeth out into light the shadow of death;
23 yana sa al’ummai su zama manya, sai kuma yă hallaka su; yana sa al’ummai su ƙasaita, yă kuma watsar da su.
He increaseth the nations, and destroyeth them; he spreadeth out the nations, and bringeth them in;
24 Yana hana shugabannin duniya ganewa; Ya bar su su yi ta makuwa, su ruɗe, su ɓata.
He taketh away the understanding of the chiefs of the people of the earth, and causeth them to wander in a pathless waste.
25 Suna lallube cikin duhu ba haske; yă sa su yi ta tangaɗi kamar bugaggu.
They grope in the dark without light, and he maketh them to stagger like a drunkard.

< Ayuba 12 >