< Ayuba 12 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Saa tog Job til Orde og svarede:
2 “Ba shakka ku ne mutanen nan, hikima za tă mutu tare da ku!
Ja, sandelig, I er de rette, med eder dør Visdommen ud!
3 Amma ni ma ina da hankali kamar ku; ba ku fi ni ba. Wane ne bai san duk waɗannan abubuwan ba?
Ogsaa jeg har som I Forstand, staar ikke tilbage for eder, hvo kender vel ikke sligt?
4 “Na zama abin dariya ga abokaina, ko da yake na yi kira ga Allah ya kuwa amsa mini, duk da haka suka yi mini riya ko da yake ni mai adalci ne kuma marar laifi!
Til Latter for Venner er den, der raabte til Gud og fik Svar, den retfærdige er til Latter.
5 Mutanen da ba su da damuwa suna jin daɗin ganin waɗanda suke dab da fāɗuwa.
I Ulykke falder de fromme, den sorgløse spotter Faren, hans Fod staar fast, mens Fristen varer.
6 Amma wurin zaman’yan fashi yana nan ba mai damunsu, waɗanda kuma suke saɓa wa Allah suna zamansu lafiya, har ma da masu ɗaukar allahnsu a hannuwansu.
I Fred er Voldsmænds Telte, og trygge er de, der vækker Guds Vrede, den, der fører Gud i sin Haand.
7 “Amma ka tambayi dabbobi, za su kuma koya maka, ko kuma tsuntsayen sararin sama kuma za su gaya maka.
Spørg dog Kvæget, det skal lære dig, Himlens Fugle, de skal oplyse dig,
8 Ko ka yi magana da duniya, za tă kuma koya maka, ko kuma ka bar kifin teku su sanar da kai.
se til Jorden, den skal lære dig lad Havets Fisk fortælle dig det!
9 Wane ne cikin waɗannan bai san cewa hannun Ubangiji ne ya yi wannan ba?
Hvem blandt dem alle ved vel ikke, at HERRENS Haand har skabt det;
10 Ran kowace halitta yana a hannunsa, haka kuma numfashin dukan’yan adam.
han holder alt levendes Sjæl i sin Haand, alt Menneskekødets Aand!
11 Ko kunne ba ya gwada kalmomi kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci?
Prøver ej Øret Ord, og smager ej Ganen Maden?
12 Ko ba a wurin tsofaffi ake samun hikima ba? Ba tsawon rai yana kawo ganewa ba?
Er Alderdom eet med Visdom, Dagenes Række med Indsigt?
13 “Allah ne mai iko da kuma hikima, shawara da ganewa nasa ne.
Hos ham er der Visdom og Vælde, hos ham er der Raad og Indsigt.
14 Abin da ya rushe ba a iya ginawa ba; in ya kulle mutum ba a iya buɗe shi a sake shi ba.
Hvad han river ned, det bygges ej op, den, han lukker inde, kommer ej ud;
15 Idan ya hana ruwan sama, za a yi fări; in kuma ya saki ruwa za a yi ambaliya.
han dæmmer for Vandet, og Tørke kommer, han slipper det løs, og det omvælter Jorden.
16 Shi ne mai ƙarfi da kuma mai nasara; mai ruɗi da wanda aka ruɗa, duk nasa ne.
Hos ham er der Kraft og Fasthed; den, der farer og fører vild, er hans Værk.
17 Yakan sa mashawarta su zama marasa hikima yă kuma sa wawaye su zama masu shari’a.
Raadsherrer fører han nøgne bort, og Dommere gør han til Taaber;
18 Yana cire sarƙar da sarakuna suka ɗaura yă kuma ɗaura musu wata tsumma a kwankwaso.
han løser, hvad Konger bandt, og binder dem Reb om Lænd;
19 Yakan ƙasƙantar da firistoci yă kuma tumɓuke masu ikon da aka kafa tun da daɗewa.
Præster fører han nøgne bort og styrter ældgamle Slægter;
20 Yana sa amintattun mashawarta su yi shiru yakan kawar da hikimar dattawa.
han røver de dygtige Mælet og tager de gamles Sans;
21 Yakan sa masu iko su ji kunya yă kuma ƙwace ƙarfin masu ƙarfi.
han udøser Haan over Fyrster og løser de stærkes Bælte;
22 Yana buɗe abubuwan da suke cikin duhu yă kuma kawo haske a wuraren da ba haske;
han drager det skjulte frem af Mørket og bringer Mulmet for Lyset,
23 yana sa al’ummai su zama manya, sai kuma yă hallaka su; yana sa al’ummai su ƙasaita, yă kuma watsar da su.
gør Folkene store og lægger dem øde, udvider Folkeslags Grænser og fører dem atter bort;
24 Yana hana shugabannin duniya ganewa; Ya bar su su yi ta makuwa, su ruɗe, su ɓata.
han tager Jordens Høvdingers Vid og lader dem rave i vejløst Øde;
25 Suna lallube cikin duhu ba haske; yă sa su yi ta tangaɗi kamar bugaggu.
de famler i Mørke uden Lys og raver omkring som drukne.

< Ayuba 12 >