< Ayuba 12 >
2 “Ba shakka ku ne mutanen nan, hikima za tă mutu tare da ku!
“Uistinu, vi ste cvijet naroda, sa vama će izumrijeti mudrost.
3 Amma ni ma ina da hankali kamar ku; ba ku fi ni ba. Wane ne bai san duk waɗannan abubuwan ba?
Al' i ja znam k'o i vi misliti, ni u čemu od vas gori nisam: tko za stvari takve ne bi znao?
4 “Na zama abin dariya ga abokaina, ko da yake na yi kira ga Allah ya kuwa amsa mini, duk da haka suka yi mini riya ko da yake ni mai adalci ne kuma marar laifi!
Prijateljima sam svojim ja na podsmijeh što zazivam Boga da mi odgovori! Na podsmijeh ja sam - pravednik neporočan!
5 Mutanen da ba su da damuwa suna jin daɗin ganin waɗanda suke dab da fāɗuwa.
Prezirat' je nesretnika - sretni misle, udariti treba onog što posrće!
6 Amma wurin zaman’yan fashi yana nan ba mai damunsu, waɗanda kuma suke saɓa wa Allah suna zamansu lafiya, har ma da masu ɗaukar allahnsu a hannuwansu.
Dotle su na miru šatori pljačkaša, izazivači Boga žive bezbrižno kao da Boga u šaci svojoj drže!
7 “Amma ka tambayi dabbobi, za su kuma koya maka, ko kuma tsuntsayen sararin sama kuma za su gaya maka.
Ali pitaj zvijeri, i poučit će te; ptice nebeske pitaj, i razjasnit će ti.
8 Ko ka yi magana da duniya, za tă kuma koya maka, ko kuma ka bar kifin teku su sanar da kai.
Gušteri zemlje to će ti protumačit', ribe u moru ispripovjedit će ti.
9 Wane ne cikin waɗannan bai san cewa hannun Ubangiji ne ya yi wannan ba?
Od stvorenja sviju, koje ne bi znalo da je sve to Božja ruka učinila?!
10 Ran kowace halitta yana a hannunsa, haka kuma numfashin dukan’yan adam.
U ruci mu leži život svakog bića i dah životvorni svakog ljudskog tijela.
11 Ko kunne ba ya gwada kalmomi kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci?
Zar uhom mi ne sudimo besjedu k'o što kušamo nepcem okus jela?
12 Ko ba a wurin tsofaffi ake samun hikima ba? Ba tsawon rai yana kawo ganewa ba?
Sjedine mudrost donose čovjeku, a s vijekom dugim umnost mu dolazi.
13 “Allah ne mai iko da kuma hikima, shawara da ganewa nasa ne.
Ali u Njemu mudrost je i snaga, u Njemu savjet je i sva razumnost.
14 Abin da ya rushe ba a iya ginawa ba; in ya kulle mutum ba a iya buɗe shi a sake shi ba.
Što razgradi, sagradit neće nitko, kog zatvori, nitko ne oslobađa.
15 Idan ya hana ruwan sama, za a yi fări; in kuma ya saki ruwa za a yi ambaliya.
Ustavi li vodu, suša nastaje; pusti li je, svu zemlju ispremetne.
16 Shi ne mai ƙarfi da kuma mai nasara; mai ruɗi da wanda aka ruɗa, duk nasa ne.
Jer u njemu je snaga i sva mudrost, njegov je prevareni i varalica.
17 Yakan sa mashawarta su zama marasa hikima yă kuma sa wawaye su zama masu shari’a.
On savjetnike lišava razbora, suce pametne udara bezumljem.
18 Yana cire sarƙar da sarakuna suka ɗaura yă kuma ɗaura musu wata tsumma a kwankwaso.
On otpasuje pojas kraljevima i užetom im vezuje bokove.
19 Yakan ƙasƙantar da firistoci yă kuma tumɓuke masu ikon da aka kafa tun da daɗewa.
On bosonoge tjera svećenike i mogućnike sa vlasti obara.
20 Yana sa amintattun mashawarta su yi shiru yakan kawar da hikimar dattawa.
On diže riječ iz usta rječitima i starcima pravo rasuđivanje.
21 Yakan sa masu iko su ji kunya yă kuma ƙwace ƙarfin masu ƙarfi.
On sasiplje prezir po plemićima i junacima bedra raspasuje.
22 Yana buɗe abubuwan da suke cikin duhu yă kuma kawo haske a wuraren da ba haske;
On dubinama razotkriva tmine i sjenu smrtnu na svjetlo izvodi.
23 yana sa al’ummai su zama manya, sai kuma yă hallaka su; yana sa al’ummai su ƙasaita, yă kuma watsar da su.
On diže narod pa ga uništava, umnoži ga a potom iskorijeni.
24 Yana hana shugabannin duniya ganewa; Ya bar su su yi ta makuwa, su ruɗe, su ɓata.
On zaluđuje vladare naroda te po bespuću lutaju pustinjskom
25 Suna lallube cikin duhu ba haske; yă sa su yi ta tangaɗi kamar bugaggu.
i pipaju u tmini bez svjetlosti glavinjajući poput pijanaca.