< Ayuba 11 >

1 Sa’an nan Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
Entonces Zofar el Naamatita respondió y dijo:
2 “Duk surutun nan ba za a amsa maka ba? Ko mai surutun nan marar laifi ne?
¿Todas estas palabras quedan sin respuesta? ¿Un hombre tiene razón porque está lleno de palabras?
3 Ko maganganun nan naka marasa amfani za su sa mutane su yi maka shiru? Ba wanda zai kwaɓe ka lokacin da kake faɗar maganar da ba daidai ba?
¿Son tus palabras de orgullo para callar a los hombres? ¿Y que nadie puede contestar a tus burlas, sin que nadie te avergüence?
4 Ka ce wa Allah, ‘Abin da na gaskata ba laifi ba ne kuma ni mai tsabta ne a gabanka.’
Puedes decir: Mi camino es limpio, y estoy libre de pecado en tus ojos.
5 Da ma Allah zai yi magana, yă buɗe baki yă faɗi wani abin da ka yi da ba daidai ba
Pero si solo Dios tomara la palabra, abriera sus labios para discutir contigo;
6 yă kuma buɗe maka asirin hikima, gama hikima ta gaskiya tana da gefe biyu. Ka san wannan, Allah ya riga ya manta da waɗansu zunubanka.
¡Y te dejaría en claro los secretos de la sabiduría y las maravillas de su propósito y que no te ha castigado de acuerdo a tu iniquidad!
7 “Ko za ka iya gane al’amuran Allah? Ko za ka iya gane girman asirin Maɗaukaki?
¿Crees que investigando vas a encontrar la perfección en Dios, que vas descubrir los límites del Dios Todopoderoso?
8 Sun fi nisan sama tudu, me za ka iya yi? Sun fi zurfin kabari zurfi, me za ka sani? (Sheol h7585)
Que puedes hacer, son más altos que el cielo; más profundo que él sepulcro, como lo conocerás; (Sheol h7585)
9 Tsayinsu ya fi tsawon duniya da kuma fāɗin teku.
Más largos en medida que la tierra, y más anchos que el mar.
10 “In ya zo ya kulle ka a kurkuku ya ce kai mai laifi ne, wa zai hana shi?
Si él se atraviesa, aprisiona o congrega, ¿quién puede impedírselo?
11 Ba shakka yana iya gane mutanen da suke marasa gaskiya; kuma in ya ga abin da yake mugu, ba ya kula ne?
Porque él sabe que los hombres son vanos; Él ve el mal y toma nota.
12 Amma daƙiƙin mutum ba ya taɓa zama mai hikima kamar dai a ce ba a taɓa haihuwar ɗan aholaki horarre.
Y así, un hombre vano obtendrá sabiduría, cuando él pollino de un asno salvaje nazca hombre.
13 “Duk da haka in ka miƙa masa zuciyarka, ka kuma miƙa hannuwanka gare shi,
He aquí sí tu corazón está firme, extiende tus manos hacia él;
14 in ka kawar da zunubin da yake hannunka, ba ka bar zunubi ya kasance tare da kai ba
Si apartas el mal de tus manos y no dejas que el mal tenga lugar en tu casa;
15 shi ne za ka iya ɗaga fuskarka ba tare da jin kunya ba; za ka tsaya da ƙarfi kuma ba za ka ji tsoro ba.
Entonces verdaderamente tu rostro será levantado, sin ninguna marca de pecado, y estarás firme en tu lugar sin temor:
16 Ba shakka za ka manta da wahalolinka, za ka tuna da su kamar yadda ruwa yake wucewa.
Porque tu dolor saldrá de tu memoria, como las aguas que fluyen:
17 Rayuwarka za tă fi hasken rana haske, duhu kuma zai zama kamar safiya.
Y tu vida será más brillante que el día; aunque esté oscuro, se volverá como la mañana.
18 Za ka zauna lafiya, domin akwai bege; za ka duba kewaye da kai ka huta cikin kwanciyar rai.
Y estarás confiado porque hay esperanza; después de mirar alrededor, confiadamente tomarás tu descanso;
19 Za ka kwanta, ba wanda zai sa ka ji tsoro, da yawa za su zo neman taimako a wurinka.
Durmiendo sin temor al peligro; y los hombres desearán tener gracia en tus ojos;
20 Amma idanun mugaye ba za su iya gani ba, kuma ba za su iya tserewa ba; begensu zai zama na mutuwa.”
Pero los ojos de los malvados se acabarán; no encontrarán refugio, y su única esperanza es la muerte.

< Ayuba 11 >