< Ayuba 11 >
1 Sa’an nan Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
Entonces Sofar naamatita respondió:
2 “Duk surutun nan ba za a amsa maka ba? Ko mai surutun nan marar laifi ne?
¿No habrá respuesta a la abundancia de palabras? ¿Será justificado el que habla mucho?
3 Ko maganganun nan naka marasa amfani za su sa mutane su yi maka shiru? Ba wanda zai kwaɓe ka lokacin da kake faɗar maganar da ba daidai ba?
¿Harán callar a los hombres tus jactancias? ¿Harás escarnio sin que alguno te avergüence?
4 Ka ce wa Allah, ‘Abin da na gaskata ba laifi ba ne kuma ni mai tsabta ne a gabanka.’
Pues dijiste: Mi enseñanza es pura, y soy inocente delante de Ti.
5 Da ma Allah zai yi magana, yă buɗe baki yă faɗi wani abin da ka yi da ba daidai ba
Pero, quién diera que ʼElohim hable y abra su boca hacia ti.
6 yă kuma buɗe maka asirin hikima, gama hikima ta gaskiya tana da gefe biyu. Ka san wannan, Allah ya riga ya manta da waɗansu zunubanka.
Te declare secretos de sabiduría, porque Él es de múltiple entendimiento. Así entenderías que ʼElohim, en tu favor, te castiga menos de lo que merece tu iniquidad.
7 “Ko za ka iya gane al’amuran Allah? Ko za ka iya gane girman asirin Maɗaukaki?
¿Descubrirás tú las profundidades de ʼElohim? ¿Puedes hallar los límites de ʼEL-Shadday?
8 Sun fi nisan sama tudu, me za ka iya yi? Sun fi zurfin kabari zurfi, me za ka sani? (Sheol )
Es más alto que los cielos, ¿qué puedes tú hacer? Es más profundo que el Seol, ¿qué puedes tú saber? (Sheol )
9 Tsayinsu ya fi tsawon duniya da kuma fāɗin teku.
Su dimensión es más extensa que la tierra y más ancha que el mar.
10 “In ya zo ya kulle ka a kurkuku ya ce kai mai laifi ne, wa zai hana shi?
Si Él pasa y aprisiona, o convoca una asamblea, ¿quién lo puede restringir?
11 Ba shakka yana iya gane mutanen da suke marasa gaskiya; kuma in ya ga abin da yake mugu, ba ya kula ne?
Porque Él conoce a los hombres vanos. Ve también su perversidad, ¿y no la considerará?
12 Amma daƙiƙin mutum ba ya taɓa zama mai hikima kamar dai a ce ba a taɓa haihuwar ɗan aholaki horarre.
El hombre vano será entendido cuando un pollino de asno montés nazca hombre.
13 “Duk da haka in ka miƙa masa zuciyarka, ka kuma miƙa hannuwanka gare shi,
Si tú dispones tu corazón y extiendes a Él tus manos,
14 in ka kawar da zunubin da yake hannunka, ba ka bar zunubi ya kasance tare da kai ba
si hay iniquidad en tus manos, la alejas de ti y no permites que la perversidad more en tus tiendas,
15 shi ne za ka iya ɗaga fuskarka ba tare da jin kunya ba; za ka tsaya da ƙarfi kuma ba za ka ji tsoro ba.
entonces levantarías tu semblante libre de mancha, estarías firme y nada temerías,
16 Ba shakka za ka manta da wahalolinka, za ka tuna da su kamar yadda ruwa yake wucewa.
olvidarías tu aflicción y la recordarías como aguas que pasaron.
17 Rayuwarka za tă fi hasken rana haske, duhu kuma zai zama kamar safiya.
Tu existencia sería más resplandeciente que el mediodía. Aunque haya oscuridad, sería como la alborada.
18 Za ka zauna lafiya, domin akwai bege; za ka duba kewaye da kai ka huta cikin kwanciyar rai.
Estarías confiado, porque habría esperanza. Mirarías alrededor y descansarías seguro,
19 Za ka kwanta, ba wanda zai sa ka ji tsoro, da yawa za su zo neman taimako a wurinka.
reposarías, sin que alguno te espante. Y muchos implorarían tu favor.
20 Amma idanun mugaye ba za su iya gani ba, kuma ba za su iya tserewa ba; begensu zai zama na mutuwa.”
Pero los ojos de los perversos fallarán, y no habrá escape para ellos. Su esperanza será el último suspiro.