< Ayuba 11 >

1 Sa’an nan Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
Отвещав же Софар Минейский, рече:
2 “Duk surutun nan ba za a amsa maka ba? Ko mai surutun nan marar laifi ne?
глаголяй много, и противоуслышит: или многоречив мнится быти праведен? Благословен рожденный от жены малолетен.
3 Ko maganganun nan naka marasa amfani za su sa mutane su yi maka shiru? Ba wanda zai kwaɓe ka lokacin da kake faɗar maganar da ba daidai ba?
Не мног во словесех буди: несть бо противовещаяй ти.
4 Ka ce wa Allah, ‘Abin da na gaskata ba laifi ba ne kuma ni mai tsabta ne a gabanka.’
Не глаголи бо, яко чист есмь делы и безпорочен пред Ним:
5 Da ma Allah zai yi magana, yă buɗe baki yă faɗi wani abin da ka yi da ba daidai ba
но како Господь возглаголет к тебе и отверзет устне Свои с тобою?
6 yă kuma buɗe maka asirin hikima, gama hikima ta gaskiya tana da gefe biyu. Ka san wannan, Allah ya riga ya manta da waɗansu zunubanka.
Потом возвестит ти силу премудрости, яко сугуб будет в сих, яже противу тебе: и тогда уразумееши, яко достойная тебе сбышася от Господа, имиже согрешил еси,
7 “Ko za ka iya gane al’amuran Allah? Ko za ka iya gane girman asirin Maɗaukaki?
или след Господень обрящеши? Или в последняя достигл еси, яже сотвори Вседержитель?
8 Sun fi nisan sama tudu, me za ka iya yi? Sun fi zurfin kabari zurfi, me za ka sani? (Sheol h7585)
Высоко небо, и что сотвориши? Глубочае же сущих во аде что веси? (Sheol h7585)
9 Tsayinsu ya fi tsawon duniya da kuma fāɗin teku.
Не должае ли меры земныя, или широты морския?
10 “In ya zo ya kulle ka a kurkuku ya ce kai mai laifi ne, wa zai hana shi?
Аще же превратит вся, кто речет Ему: что сотворил еси?
11 Ba shakka yana iya gane mutanen da suke marasa gaskiya; kuma in ya ga abin da yake mugu, ba ya kula ne?
Той бо весть дела беззаконных: видев же нелепая, не презрит.
12 Amma daƙiƙin mutum ba ya taɓa zama mai hikima kamar dai a ce ba a taɓa haihuwar ɗan aholaki horarre.
Человек же инако обилует словесы: земный же рожденный от жены равен ослу пустынному.
13 “Duk da haka in ka miƙa masa zuciyarka, ka kuma miƙa hannuwanka gare shi,
Аще бо ты чисто положил еси сердце твое, воздеваеши же руце твои к Нему,
14 in ka kawar da zunubin da yake hannunka, ba ka bar zunubi ya kasance tare da kai ba
аще беззаконно что есть в руку твоею, далече сотвори е от тебе, неправда же в жилищи твоем да не вселится:
15 shi ne za ka iya ɗaga fuskarka ba tare da jin kunya ba; za ka tsaya da ƙarfi kuma ba za ka ji tsoro ba.
тако бо ти возсияет лице, якоже вода чиста: совлечешися же скверны, и не убоишися,
16 Ba shakka za ka manta da wahalolinka, za ka tuna da su kamar yadda ruwa yake wucewa.
и труда забудеши, якоже волны мимошедшия, и не устрашишися.
17 Rayuwarka za tă fi hasken rana haske, duhu kuma zai zama kamar safiya.
Молитва же твоя, аки денница, и паче полудне возсияет ти жизнь:
18 Za ka zauna lafiya, domin akwai bege; za ka duba kewaye da kai ka huta cikin kwanciyar rai.
уповая же будеши, яко будет ти надежда: от туги же и попечения явится ти мир:
19 Za ka kwanta, ba wanda zai sa ka ji tsoro, da yawa za su zo neman taimako a wurinka.
упокоишися бо, и не будет боряй тя: пременяющиися же мнози имут просити тя,
20 Amma idanun mugaye ba za su iya gani ba, kuma ba za su iya tserewa ba; begensu zai zama na mutuwa.”
спасение же оставит их: надежда бо их пагуба, очи же нечестивых истают.

< Ayuba 11 >