< Ayuba 11 >
1 Sa’an nan Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
А Софар Намаћанин одговори и рече:
2 “Duk surutun nan ba za a amsa maka ba? Ko mai surutun nan marar laifi ne?
Зар на многе речи нема одговора? Или ће човек говорљив остати прав?
3 Ko maganganun nan naka marasa amfani za su sa mutane su yi maka shiru? Ba wanda zai kwaɓe ka lokacin da kake faɗar maganar da ba daidai ba?
Хоће ли твоје лажи ућуткати људе? И кад се ругаш, зар те неће нико посрамити?
4 Ka ce wa Allah, ‘Abin da na gaskata ba laifi ba ne kuma ni mai tsabta ne a gabanka.’
Јер си рекао: Чиста је наука моја, и чист сам пред очима твојим.
5 Da ma Allah zai yi magana, yă buɗe baki yă faɗi wani abin da ka yi da ba daidai ba
Али кад би Бог проговорио и усне своје отворио на те,
6 yă kuma buɗe maka asirin hikima, gama hikima ta gaskiya tana da gefe biyu. Ka san wannan, Allah ya riga ya manta da waɗansu zunubanka.
И показао ти тајне мудрости, јер их је двојином више, познао би да те Бог кара мање него што заслужује твоје безакоње.
7 “Ko za ka iya gane al’amuran Allah? Ko za ka iya gane girman asirin Maɗaukaki?
Можеш ли ти тајне Божије докучити, или докучити савршенство Свемогућег?
8 Sun fi nisan sama tudu, me za ka iya yi? Sun fi zurfin kabari zurfi, me za ka sani? (Sheol )
То су висине небеске, шта ћеш учинити? Дубље је од пакла, како ћеш познати? (Sheol )
9 Tsayinsu ya fi tsawon duniya da kuma fāɗin teku.
Дуже од земље, шире од мора.
10 “In ya zo ya kulle ka a kurkuku ya ce kai mai laifi ne, wa zai hana shi?
Да преврати, или затвори или сабере, ко ће Му бранити?
11 Ba shakka yana iya gane mutanen da suke marasa gaskiya; kuma in ya ga abin da yake mugu, ba ya kula ne?
Јер зна ништавило људско, и видећи неваљалство зар неће пазити?
12 Amma daƙiƙin mutum ba ya taɓa zama mai hikima kamar dai a ce ba a taɓa haihuwar ɗan aholaki horarre.
Човек безуман постаје разуман, премда се човек рађа као дивље магаре.
13 “Duk da haka in ka miƙa masa zuciyarka, ka kuma miƙa hannuwanka gare shi,
Да ти управиш срце своје и подигнеш руке своје к Њему,
14 in ka kawar da zunubin da yake hannunka, ba ka bar zunubi ya kasance tare da kai ba
Ако је безакоње у руци твојој, да га уклониш, и не даш да неправда буде у шаторима твојим,
15 shi ne za ka iya ɗaga fuskarka ba tare da jin kunya ba; za ka tsaya da ƙarfi kuma ba za ka ji tsoro ba.
Тада ћеш подигнути лице своје без мане и стајаћеш тврдо и нећеш се бојати;
16 Ba shakka za ka manta da wahalolinka, za ka tuna da su kamar yadda ruwa yake wucewa.
Заборавићеш муку, као воде која протече опомињаћеш је се;
17 Rayuwarka za tă fi hasken rana haske, duhu kuma zai zama kamar safiya.
Настаће ти време ведрије него подне, синућеш, бићеш као јутро;
18 Za ka zauna lafiya, domin akwai bege; za ka duba kewaye da kai ka huta cikin kwanciyar rai.
Уздаћеш се имајући надање, закопаћеш се, и мирно ћеш спавати.
19 Za ka kwanta, ba wanda zai sa ka ji tsoro, da yawa za su zo neman taimako a wurinka.
Лежаћеш, и нико те неће плашити, и многи ће ти се молити.
20 Amma idanun mugaye ba za su iya gani ba, kuma ba za su iya tserewa ba; begensu zai zama na mutuwa.”
Али очи ће безбожницима ишчилети, и уточишта им неће бити, и надање ће им бити издисање.