< Ayuba 11 >

1 Sa’an nan Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
respondens autem Sophar Naamathites dixit
2 “Duk surutun nan ba za a amsa maka ba? Ko mai surutun nan marar laifi ne?
numquid qui multa loquitur non et audiet aut vir verbosus iustificabitur
3 Ko maganganun nan naka marasa amfani za su sa mutane su yi maka shiru? Ba wanda zai kwaɓe ka lokacin da kake faɗar maganar da ba daidai ba?
tibi soli tacebunt homines et cum ceteros inriseris a nullo confutaberis
4 Ka ce wa Allah, ‘Abin da na gaskata ba laifi ba ne kuma ni mai tsabta ne a gabanka.’
dixisti enim purus est sermo meus et mundus sum in conspectu tuo
5 Da ma Allah zai yi magana, yă buɗe baki yă faɗi wani abin da ka yi da ba daidai ba
atque utinam Deus loqueretur tecum et aperiret labia sua tibi
6 yă kuma buɗe maka asirin hikima, gama hikima ta gaskiya tana da gefe biyu. Ka san wannan, Allah ya riga ya manta da waɗansu zunubanka.
ut ostenderet tibi secreta sapientiae et quod multiplex esset lex eius et intellegeres quod multo minora exigaris a Deo quam meretur iniquitas tua
7 “Ko za ka iya gane al’amuran Allah? Ko za ka iya gane girman asirin Maɗaukaki?
forsitan vestigia Dei conprehendes et usque ad perfectum Omnipotentem repperies
8 Sun fi nisan sama tudu, me za ka iya yi? Sun fi zurfin kabari zurfi, me za ka sani? (Sheol h7585)
excelsior caelo est et quid facies profundior inferno et unde cognosces (Sheol h7585)
9 Tsayinsu ya fi tsawon duniya da kuma fāɗin teku.
longior terrae mensura eius et latior mari
10 “In ya zo ya kulle ka a kurkuku ya ce kai mai laifi ne, wa zai hana shi?
si subverterit omnia vel in unum coartaverit quis contradicet ei
11 Ba shakka yana iya gane mutanen da suke marasa gaskiya; kuma in ya ga abin da yake mugu, ba ya kula ne?
ipse enim novit hominum vanitatem et videns iniquitatem nonne considerat
12 Amma daƙiƙin mutum ba ya taɓa zama mai hikima kamar dai a ce ba a taɓa haihuwar ɗan aholaki horarre.
vir vanus in superbiam erigitur et tamquam pullum onagri se liberum natum putat
13 “Duk da haka in ka miƙa masa zuciyarka, ka kuma miƙa hannuwanka gare shi,
tu autem firmasti cor tuum et expandisti ad eum manus tuas
14 in ka kawar da zunubin da yake hannunka, ba ka bar zunubi ya kasance tare da kai ba
si iniquitatem quod est in manu tua abstuleris a te et non manserit in tabernaculo tuo iniustitia
15 shi ne za ka iya ɗaga fuskarka ba tare da jin kunya ba; za ka tsaya da ƙarfi kuma ba za ka ji tsoro ba.
tum levare poteris faciem tuam absque macula et eris stabilis et non timebis
16 Ba shakka za ka manta da wahalolinka, za ka tuna da su kamar yadda ruwa yake wucewa.
miseriae quoque oblivisceris et quasi aquarum quae praeterierint recordaberis
17 Rayuwarka za tă fi hasken rana haske, duhu kuma zai zama kamar safiya.
et quasi meridianus fulgor consurget tibi ad vesperam et cum te consumptum putaveris orieris ut lucifer
18 Za ka zauna lafiya, domin akwai bege; za ka duba kewaye da kai ka huta cikin kwanciyar rai.
et habebis fiduciam proposita tibi spe et defossus securus dormies
19 Za ka kwanta, ba wanda zai sa ka ji tsoro, da yawa za su zo neman taimako a wurinka.
requiesces et non erit qui te exterreat et deprecabuntur faciem tuam plurimi
20 Amma idanun mugaye ba za su iya gani ba, kuma ba za su iya tserewa ba; begensu zai zama na mutuwa.”
oculi autem impiorum deficient et effugium peribit ab eis et spes eorum abominatio animae

< Ayuba 11 >