< Ayuba 11 >

1 Sa’an nan Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
Allora Tsofar di Naama rispose e disse:
2 “Duk surutun nan ba za a amsa maka ba? Ko mai surutun nan marar laifi ne?
“Cotesta abbondanza di parole rimarrà ella senza risposta? Basterà egli esser loquace per aver ragione?
3 Ko maganganun nan naka marasa amfani za su sa mutane su yi maka shiru? Ba wanda zai kwaɓe ka lokacin da kake faɗar maganar da ba daidai ba?
Varranno le tue ciance a far tacere la gente? Farai tu il beffardo, senza che alcuno ti confonda?
4 Ka ce wa Allah, ‘Abin da na gaskata ba laifi ba ne kuma ni mai tsabta ne a gabanka.’
Tu dici a Dio: “Quel che sostengo è giusto, e io sono puro nel tuo cospetto”.
5 Da ma Allah zai yi magana, yă buɗe baki yă faɗi wani abin da ka yi da ba daidai ba
Ma, oh se Iddio volesse parlare e aprir la bocca per risponderti
6 yă kuma buɗe maka asirin hikima, gama hikima ta gaskiya tana da gefe biyu. Ka san wannan, Allah ya riga ya manta da waɗansu zunubanka.
e rivelarti i segreti della sua sapienza poiché infinita è la sua intelligenza vedresti allora come Iddio dimentichi parte della colpa tua.
7 “Ko za ka iya gane al’amuran Allah? Ko za ka iya gane girman asirin Maɗaukaki?
Puoi tu scandagliare le profondità di Dio? arrivare a conoscere appieno l’Onnipotente?
8 Sun fi nisan sama tudu, me za ka iya yi? Sun fi zurfin kabari zurfi, me za ka sani? (Sheol h7585)
Si tratta di cose più alte del cielo… e tu che faresti? di cose più profonde del soggiorno de’ morti… come le conosceresti? (Sheol h7585)
9 Tsayinsu ya fi tsawon duniya da kuma fāɗin teku.
La lor misura è più lunga della terra, più larga del mare.
10 “In ya zo ya kulle ka a kurkuku ya ce kai mai laifi ne, wa zai hana shi?
Se Dio passa, se incarcera, se chiama in giudizio, chi s’opporrà?
11 Ba shakka yana iya gane mutanen da suke marasa gaskiya; kuma in ya ga abin da yake mugu, ba ya kula ne?
Poich’egli conosce gli uomini perversi, scopre senza sforzo l’iniquità.
12 Amma daƙiƙin mutum ba ya taɓa zama mai hikima kamar dai a ce ba a taɓa haihuwar ɗan aholaki horarre.
Ma l’insensato diventerà savio, quando un puledro d’onàgro diventerà uomo.
13 “Duk da haka in ka miƙa masa zuciyarka, ka kuma miƙa hannuwanka gare shi,
Tu, però, se ben disponi il cuore, e protendi verso Dio le palme,
14 in ka kawar da zunubin da yake hannunka, ba ka bar zunubi ya kasance tare da kai ba
se allontani il male ch’è nelle tue mani, e non alberghi l’iniquità nelle tue tende,
15 shi ne za ka iya ɗaga fuskarka ba tare da jin kunya ba; za ka tsaya da ƙarfi kuma ba za ka ji tsoro ba.
allora alzerai la fronte senza macchia, sarai incrollabile, e non avrai paura di nulla;
16 Ba shakka za ka manta da wahalolinka, za ka tuna da su kamar yadda ruwa yake wucewa.
dimenticherai i tuoi affanni; te ne ricorderai come d’acqua passata;
17 Rayuwarka za tă fi hasken rana haske, duhu kuma zai zama kamar safiya.
la tua vita sorgerà più fulgida del meriggio, l’oscurità sarà come la luce del mattino.
18 Za ka zauna lafiya, domin akwai bege; za ka duba kewaye da kai ka huta cikin kwanciyar rai.
Sarai fiducioso perché avrai speranza; ti guarderai bene attorno e ti coricherai sicuro.
19 Za ka kwanta, ba wanda zai sa ka ji tsoro, da yawa za su zo neman taimako a wurinka.
Ti metterai a giacere e niuno ti spaventerà; e molti cercheranno il tuo favore.
20 Amma idanun mugaye ba za su iya gani ba, kuma ba za su iya tserewa ba; begensu zai zama na mutuwa.”
Ma gli occhi degli empi verranno meno; non vi sarà più rifugio per loro, e non avranno altra speranza che di esalar l’anima”.

< Ayuba 11 >