< Ayuba 11 >
1 Sa’an nan Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
Alors Tsophar, de Naama, prit la parole, et dit:
2 “Duk surutun nan ba za a amsa maka ba? Ko mai surutun nan marar laifi ne?
Ne répondra-t-on point à tant de discours, et suffira-t-il d'être un grand parleur pour être justifié?
3 Ko maganganun nan naka marasa amfani za su sa mutane su yi maka shiru? Ba wanda zai kwaɓe ka lokacin da kake faɗar maganar da ba daidai ba?
Tes vains propos feront-ils taire les gens? Te moqueras-tu, sans que personne te confonde?
4 Ka ce wa Allah, ‘Abin da na gaskata ba laifi ba ne kuma ni mai tsabta ne a gabanka.’
Tu as dit: Ma doctrine est pure, je suis sans tache devant tes yeux.
5 Da ma Allah zai yi magana, yă buɗe baki yă faɗi wani abin da ka yi da ba daidai ba
Mais je voudrais que Dieu parlât, et qu'il ouvrît sa bouche pour te répondre;
6 yă kuma buɗe maka asirin hikima, gama hikima ta gaskiya tana da gefe biyu. Ka san wannan, Allah ya riga ya manta da waɗansu zunubanka.
Qu'il te montrât les secrets de sa sagesse, de son immense sagesse; et tu reconnaîtrais que Dieu oublie une partie de ton iniquité.
7 “Ko za ka iya gane al’amuran Allah? Ko za ka iya gane girman asirin Maɗaukaki?
Trouveras-tu le fond de Dieu? Trouveras-tu la limite du Tout-Puissant?
8 Sun fi nisan sama tudu, me za ka iya yi? Sun fi zurfin kabari zurfi, me za ka sani? (Sheol )
Ce sont les hauteurs des cieux: qu'y feras-tu? C'est plus profond que les enfers: qu'y connaîtras-tu? (Sheol )
9 Tsayinsu ya fi tsawon duniya da kuma fāɗin teku.
Son étendue est plus longue que la terre, et plus large que la mer.
10 “In ya zo ya kulle ka a kurkuku ya ce kai mai laifi ne, wa zai hana shi?
S'il saisit, s'il emprisonne, s'il assemble le tribunal, qui l'en empêchera?
11 Ba shakka yana iya gane mutanen da suke marasa gaskiya; kuma in ya ga abin da yake mugu, ba ya kula ne?
Car il connaît, lui, les hommes de rien; il voit l'iniquité, sans qu'elle s'en doute;
12 Amma daƙiƙin mutum ba ya taɓa zama mai hikima kamar dai a ce ba a taɓa haihuwar ɗan aholaki horarre.
Mais l'homme vide de sens de-viendra intelligent, quand l'ânon sauvage naîtra comme un homme!
13 “Duk da haka in ka miƙa masa zuciyarka, ka kuma miƙa hannuwanka gare shi,
Si tu disposes bien ton cœur, et si tu étends tes mains vers Dieu,
14 in ka kawar da zunubin da yake hannunka, ba ka bar zunubi ya kasance tare da kai ba
(Si l'iniquité est en tes mains, éloigne-la, et que le crime n'habite point dans tes tentes! )
15 shi ne za ka iya ɗaga fuskarka ba tare da jin kunya ba; za ka tsaya da ƙarfi kuma ba za ka ji tsoro ba.
Alors certainement tu lèveras ton front sans tache; tu seras raffermi et tu ne craindras rien;
16 Ba shakka za ka manta da wahalolinka, za ka tuna da su kamar yadda ruwa yake wucewa.
Tu oublieras tes peines, tu t'en souviendras comme des eaux écoulées.
17 Rayuwarka za tă fi hasken rana haske, duhu kuma zai zama kamar safiya.
La vie se lèvera pour toi plus brillante que le midi, et l'obscurité même sera comme le matin.
18 Za ka zauna lafiya, domin akwai bege; za ka duba kewaye da kai ka huta cikin kwanciyar rai.
Tu seras plein de confiance, parce que tu auras lieu d'espérer; tu exploreras autour de toi, et tu te coucheras en sécurité;
19 Za ka kwanta, ba wanda zai sa ka ji tsoro, da yawa za su zo neman taimako a wurinka.
Tu t'étendras à ton aise, et nul ne t'effraiera; et bien des gens te feront la cour.
20 Amma idanun mugaye ba za su iya gani ba, kuma ba za su iya tserewa ba; begensu zai zama na mutuwa.”
Mais les yeux des méchants seront consumés; tout refuge leur sera ôté, et toute leur espérance sera de rendre l'âme.