< Ayuba 11 >
1 Sa’an nan Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
Alors Zophar, le Naamathite, prit la parole,
2 “Duk surutun nan ba za a amsa maka ba? Ko mai surutun nan marar laifi ne?
« Ne faut-il pas répondre à la multitude de mots? Un homme plein de paroles doit-il être justifié?
3 Ko maganganun nan naka marasa amfani za su sa mutane su yi maka shiru? Ba wanda zai kwaɓe ka lokacin da kake faɗar maganar da ba daidai ba?
Vos fanfaronnades devraient-elles inciter les hommes à se taire? Quand tu te moques, personne ne te fait honte?
4 Ka ce wa Allah, ‘Abin da na gaskata ba laifi ba ne kuma ni mai tsabta ne a gabanka.’
Car vous dites: « Ma doctrine est pure ». Je suis propre à vos yeux.
5 Da ma Allah zai yi magana, yă buɗe baki yă faɗi wani abin da ka yi da ba daidai ba
Mais oh, que Dieu parle, et ouvrir ses lèvres contre toi,
6 yă kuma buɗe maka asirin hikima, gama hikima ta gaskiya tana da gefe biyu. Ka san wannan, Allah ya riga ya manta da waɗansu zunubanka.
qu'il te montre les secrets de la sagesse! Car la vraie sagesse a deux côtés. Sachez donc que Dieu exige de vous moins que ce que votre iniquité mérite.
7 “Ko za ka iya gane al’amuran Allah? Ko za ka iya gane girman asirin Maɗaukaki?
« Pouvez-vous sonder le mystère de Dieu? Ou pouvez-vous sonder les limites du Tout-Puissant?
8 Sun fi nisan sama tudu, me za ka iya yi? Sun fi zurfin kabari zurfi, me za ka sani? (Sheol )
Ils sont hauts comme le ciel. Que pouvez-vous faire? Ils sont plus profonds que le Sheol. Que pouvez-vous savoir? (Sheol )
9 Tsayinsu ya fi tsawon duniya da kuma fāɗin teku.
Sa mesure est plus longue que la terre, et plus large que la mer.
10 “In ya zo ya kulle ka a kurkuku ya ce kai mai laifi ne, wa zai hana shi?
S'il passe, ou s'il enferme, ou convoque un tribunal, alors qui peut s'opposer à lui?
11 Ba shakka yana iya gane mutanen da suke marasa gaskiya; kuma in ya ga abin da yake mugu, ba ya kula ne?
Car il connaît les faux hommes. Il voit aussi l'iniquité, même s'il ne la considère pas.
12 Amma daƙiƙin mutum ba ya taɓa zama mai hikima kamar dai a ce ba a taɓa haihuwar ɗan aholaki horarre.
Un homme à la tête vide devient sage quand un homme naît comme le petit d'une ânesse sauvage.
13 “Duk da haka in ka miƙa masa zuciyarka, ka kuma miƙa hannuwanka gare shi,
« Si tu mets ton cœur à l'endroit, tendez vos mains vers lui.
14 in ka kawar da zunubin da yake hannunka, ba ka bar zunubi ya kasance tare da kai ba
Si l'iniquité est dans ta main, éloigne-la. Ne laissez pas l'iniquité habiter dans vos tentes.
15 shi ne za ka iya ɗaga fuskarka ba tare da jin kunya ba; za ka tsaya da ƙarfi kuma ba za ka ji tsoro ba.
Alors tu lèveras ton visage sans tache. Oui, vous serez inébranlables, et vous ne craindrez pas,
16 Ba shakka za ka manta da wahalolinka, za ka tuna da su kamar yadda ruwa yake wucewa.
car tu oublieras ta misère. Vous vous en souviendrez comme des eaux qui sont passées.
17 Rayuwarka za tă fi hasken rana haske, duhu kuma zai zama kamar safiya.
La vie sera plus claire que l'aurore. Même s'il y a des ténèbres, ce sera comme le matin.
18 Za ka zauna lafiya, domin akwai bege; za ka duba kewaye da kai ka huta cikin kwanciyar rai.
Vous serez en sécurité, car il y a de l'espoir. Oui, vous chercherez, et vous vous reposerez en sécurité.
19 Za ka kwanta, ba wanda zai sa ka ji tsoro, da yawa za su zo neman taimako a wurinka.
Tu te coucheras aussi, et personne ne te fera peur. Oui, beaucoup vont vous courtiser.
20 Amma idanun mugaye ba za su iya gani ba, kuma ba za su iya tserewa ba; begensu zai zama na mutuwa.”
Mais les yeux des méchants se perdront. Ils n'auront aucun moyen de fuir. Leur espoir sera l'abandon de l'esprit. »