< Ayuba 11 >

1 Sa’an nan Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
Then Sophar the Naamathite answered, and said:
2 “Duk surutun nan ba za a amsa maka ba? Ko mai surutun nan marar laifi ne?
Shall not he that speaketh much, hear also? or shall a man full of talk be justified?
3 Ko maganganun nan naka marasa amfani za su sa mutane su yi maka shiru? Ba wanda zai kwaɓe ka lokacin da kake faɗar maganar da ba daidai ba?
Shall men hold their peace to thee only? and when thou hast mocked others, shall no man confute thee?
4 Ka ce wa Allah, ‘Abin da na gaskata ba laifi ba ne kuma ni mai tsabta ne a gabanka.’
For thou hast said: My word is pure, and I am clean in thy sight.
5 Da ma Allah zai yi magana, yă buɗe baki yă faɗi wani abin da ka yi da ba daidai ba
And I wish that God would speak with thee, and would open his lips to thee,
6 yă kuma buɗe maka asirin hikima, gama hikima ta gaskiya tana da gefe biyu. Ka san wannan, Allah ya riga ya manta da waɗansu zunubanka.
That he might shew thee the secrets of wisdom, and that his law is manifold, and thou mightest understand that he exacteth much less of thee, than thy iniquity deserveth.
7 “Ko za ka iya gane al’amuran Allah? Ko za ka iya gane girman asirin Maɗaukaki?
Peradventure thou wilt comprehend the steps of God, and wilt find out the Almighty perfectly?
8 Sun fi nisan sama tudu, me za ka iya yi? Sun fi zurfin kabari zurfi, me za ka sani? (Sheol h7585)
He is higher than heaven, and what wilt thou do? he is deeper than hell, and how wilt thou know? (Sheol h7585)
9 Tsayinsu ya fi tsawon duniya da kuma fāɗin teku.
The measure of him is longer than the earth, and broader than the sea.
10 “In ya zo ya kulle ka a kurkuku ya ce kai mai laifi ne, wa zai hana shi?
If he shall overturn all things, or shall press them together, who shall contradict him?
11 Ba shakka yana iya gane mutanen da suke marasa gaskiya; kuma in ya ga abin da yake mugu, ba ya kula ne?
For he knoweth the vanity of men, and when he seeth iniquity, doth he not consider it?
12 Amma daƙiƙin mutum ba ya taɓa zama mai hikima kamar dai a ce ba a taɓa haihuwar ɗan aholaki horarre.
A vain man is lifted up into pride, and thinketh himself born free like a wild ass’s colt.
13 “Duk da haka in ka miƙa masa zuciyarka, ka kuma miƙa hannuwanka gare shi,
Rut thou hast hardened thy heart, and hast spread thy hands to him.
14 in ka kawar da zunubin da yake hannunka, ba ka bar zunubi ya kasance tare da kai ba
If thou wilt put away from thee the iniquity that is in thy hand, and lot not injustice remain in thy tabernacle:
15 shi ne za ka iya ɗaga fuskarka ba tare da jin kunya ba; za ka tsaya da ƙarfi kuma ba za ka ji tsoro ba.
Then mayst thou lift up thy face without spot, and thou shalt be steadfast, and shalt not fear.
16 Ba shakka za ka manta da wahalolinka, za ka tuna da su kamar yadda ruwa yake wucewa.
Thou shalt also forget misery, and remember it only as waters that are passed away.
17 Rayuwarka za tă fi hasken rana haske, duhu kuma zai zama kamar safiya.
And brightness like that of the noonday, shall arise to thee at evening: and when thou shalt think thyself consumed, thou shalt rise as the day star.
18 Za ka zauna lafiya, domin akwai bege; za ka duba kewaye da kai ka huta cikin kwanciyar rai.
And thou shalt have confidence, hope being set before thee, and being buried thou shalt sleep secure.
19 Za ka kwanta, ba wanda zai sa ka ji tsoro, da yawa za su zo neman taimako a wurinka.
Thou shalt rest, and there shall be none to make thee afraid: and many shall entreat thy face.
20 Amma idanun mugaye ba za su iya gani ba, kuma ba za su iya tserewa ba; begensu zai zama na mutuwa.”
But the eyes of the wicked shall decay, and the way to escape shall fail them, and their hope the abomination of the soul.

< Ayuba 11 >