< Ayuba 11 >

1 Sa’an nan Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
And Zophar the Naamathite answered and said,
2 “Duk surutun nan ba za a amsa maka ba? Ko mai surutun nan marar laifi ne?
Should not the multitude of words be answered? and should a man of much talk be justified?
3 Ko maganganun nan naka marasa amfani za su sa mutane su yi maka shiru? Ba wanda zai kwaɓe ka lokacin da kake faɗar maganar da ba daidai ba?
Should thy fictions make men hold their peace? and shouldest thou mock, and no one make [thee] ashamed?
4 Ka ce wa Allah, ‘Abin da na gaskata ba laifi ba ne kuma ni mai tsabta ne a gabanka.’
For thou sayest, My doctrine is pure, and I am clean in thine eyes.
5 Da ma Allah zai yi magana, yă buɗe baki yă faɗi wani abin da ka yi da ba daidai ba
But oh that God would speak, and open his lips against thee;
6 yă kuma buɗe maka asirin hikima, gama hikima ta gaskiya tana da gefe biyu. Ka san wannan, Allah ya riga ya manta da waɗansu zunubanka.
And that he would shew thee the secrets of wisdom, how that they are the double of what is realised; and know that God passeth by [much] of thine iniquity!
7 “Ko za ka iya gane al’amuran Allah? Ko za ka iya gane girman asirin Maɗaukaki?
Canst thou by searching find out God? canst thou find out the Almighty to perfection?
8 Sun fi nisan sama tudu, me za ka iya yi? Sun fi zurfin kabari zurfi, me za ka sani? (Sheol h7585)
[It is as] the heights of heaven; what wilt thou do? deeper than Sheol; what canst thou know? (Sheol h7585)
9 Tsayinsu ya fi tsawon duniya da kuma fāɗin teku.
The measure thereof is longer than the earth, and broader than the sea.
10 “In ya zo ya kulle ka a kurkuku ya ce kai mai laifi ne, wa zai hana shi?
If he pass by, and shut up, and call to judgment, who can hinder him?
11 Ba shakka yana iya gane mutanen da suke marasa gaskiya; kuma in ya ga abin da yake mugu, ba ya kula ne?
For he knoweth vain men, and seeth wickedness when [man] doth not consider it;
12 Amma daƙiƙin mutum ba ya taɓa zama mai hikima kamar dai a ce ba a taɓa haihuwar ɗan aholaki horarre.
Yet a senseless man will make bold, though man be born [like] the foal of a wild ass.
13 “Duk da haka in ka miƙa masa zuciyarka, ka kuma miƙa hannuwanka gare shi,
If thou prepare thy heart and stretch out thy hands toward him,
14 in ka kawar da zunubin da yake hannunka, ba ka bar zunubi ya kasance tare da kai ba
If thou put far away the iniquity which is in thy hand, and let not wrong dwell in thy tents;
15 shi ne za ka iya ɗaga fuskarka ba tare da jin kunya ba; za ka tsaya da ƙarfi kuma ba za ka ji tsoro ba.
Surely then shalt thou lift up thy face without spot, and thou shalt be stedfast and shalt not fear:
16 Ba shakka za ka manta da wahalolinka, za ka tuna da su kamar yadda ruwa yake wucewa.
For thou shalt forget misery; as waters that are passed away shalt thou remember it;
17 Rayuwarka za tă fi hasken rana haske, duhu kuma zai zama kamar safiya.
And life shall arise brighter than noonday; though thou be enshrouded in darkness, thou shalt be as the morning,
18 Za ka zauna lafiya, domin akwai bege; za ka duba kewaye da kai ka huta cikin kwanciyar rai.
And thou shalt have confidence, because there shall be hope; and having searched about [thee], thou shalt take rest in safety.
19 Za ka kwanta, ba wanda zai sa ka ji tsoro, da yawa za su zo neman taimako a wurinka.
Yea, thou shalt lie down, and none shall make thee afraid; and many shall seek thy favour.
20 Amma idanun mugaye ba za su iya gani ba, kuma ba za su iya tserewa ba; begensu zai zama na mutuwa.”
But the eyes of the wicked shall fail, and [all] refuge shall vanish from them, and their hope [shall be] the breathing out of life.

< Ayuba 11 >