< Ayuba 11 >

1 Sa’an nan Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
Then Zophar the Naamathite replied:
2 “Duk surutun nan ba za a amsa maka ba? Ko mai surutun nan marar laifi ne?
“Should this stream of words go unanswered and such a speaker be vindicated?
3 Ko maganganun nan naka marasa amfani za su sa mutane su yi maka shiru? Ba wanda zai kwaɓe ka lokacin da kake faɗar maganar da ba daidai ba?
Should your babbling put others to silence? Will you scoff without rebuke?
4 Ka ce wa Allah, ‘Abin da na gaskata ba laifi ba ne kuma ni mai tsabta ne a gabanka.’
You have said, ‘My doctrine is sound, and I am pure in Your sight.’
5 Da ma Allah zai yi magana, yă buɗe baki yă faɗi wani abin da ka yi da ba daidai ba
But if only God would speak and open His lips against you,
6 yă kuma buɗe maka asirin hikima, gama hikima ta gaskiya tana da gefe biyu. Ka san wannan, Allah ya riga ya manta da waɗansu zunubanka.
and disclose to you the secrets of wisdom, for true wisdom has two sides. Know then that God exacts from you less than your iniquity deserves.
7 “Ko za ka iya gane al’amuran Allah? Ko za ka iya gane girman asirin Maɗaukaki?
Can you fathom the deep things of God or discover the limits of the Almighty?
8 Sun fi nisan sama tudu, me za ka iya yi? Sun fi zurfin kabari zurfi, me za ka sani? (Sheol h7585)
They are higher than the heavens—what can you do? They are deeper than Sheol—what can you know? (Sheol h7585)
9 Tsayinsu ya fi tsawon duniya da kuma fāɗin teku.
Their measure is longer than the earth and wider than the sea.
10 “In ya zo ya kulle ka a kurkuku ya ce kai mai laifi ne, wa zai hana shi?
If He comes along to imprison you, or convenes a court, who can stop Him?
11 Ba shakka yana iya gane mutanen da suke marasa gaskiya; kuma in ya ga abin da yake mugu, ba ya kula ne?
Surely He knows the deceit of men. If He sees iniquity, does He not take note?
12 Amma daƙiƙin mutum ba ya taɓa zama mai hikima kamar dai a ce ba a taɓa haihuwar ɗan aholaki horarre.
But a witless man can no more become wise than the colt of a wild donkey can be born a man!
13 “Duk da haka in ka miƙa masa zuciyarka, ka kuma miƙa hannuwanka gare shi,
As for you, if you direct your heart and lift up your hands to Him,
14 in ka kawar da zunubin da yake hannunka, ba ka bar zunubi ya kasance tare da kai ba
if you put away the iniquity in your hand, and allow no injustice to dwell in your tents,
15 shi ne za ka iya ɗaga fuskarka ba tare da jin kunya ba; za ka tsaya da ƙarfi kuma ba za ka ji tsoro ba.
then indeed you will lift up your face without shame; you will stand firm and unafraid.
16 Ba shakka za ka manta da wahalolinka, za ka tuna da su kamar yadda ruwa yake wucewa.
For you will forget your misery, recalling it only as waters gone by.
17 Rayuwarka za tă fi hasken rana haske, duhu kuma zai zama kamar safiya.
Your life will be brighter than noonday; its darkness will be like the morning.
18 Za ka zauna lafiya, domin akwai bege; za ka duba kewaye da kai ka huta cikin kwanciyar rai.
You will be secure, because there is hope, and you will look around and lie down in safety.
19 Za ka kwanta, ba wanda zai sa ka ji tsoro, da yawa za su zo neman taimako a wurinka.
You will lie down without fear, and many will court your favor.
20 Amma idanun mugaye ba za su iya gani ba, kuma ba za su iya tserewa ba; begensu zai zama na mutuwa.”
But the eyes of the wicked will fail, and escape will elude them; they will hope for their last breath.”

< Ayuba 11 >