< Ayuba 10 >

1 “Na gaji da rayuwa; saboda haka bari in faɗi zuciyata gabagadi yadda raina yake jin ba daɗi.
Mi alma es cortada en mi vida: por tanto yo soltaré mi queja sobre mí, y hablaré con amargura de mi alma.
2 Zan ce wa Allah, kada ka hukunta ni, amma ka gaya mini laifin da na yi maka.
Diré a Dios: No me condenes: házme entender por qué pleitéas conmigo.
3 Kana jin daɗin ba ni wahala, don me ka yashe ni, abin da ka halitta da hannunka, yayinda kake murmushi game da shirye-shiryen mugaye?
¿Parécete bien que oprimas, y que deseches la obra de tus manos, y que favorezcas el consejo de los impíos?
4 Idanunka irin na mutum ne? Kana gani yadda mutum yake gani ne?
¿Tienes tú ojos de carne? ¿ves tú como el hombre?
5 Kwanakinka kamar na mutane ne, ko shekarunka kamar na mutane ne
¿Tus días son como los días del hombre? ¿tus años son como los tiempos humanos,
6 da za ka neme ni da laifi ka hukunta ni?
Que inquieras mi iniquidad, y busques mi pecado?
7 Ko da yake ka san ba ni da laifi, kuma ba wanda zai iya cetona daga hannunka.
Sobre saber tú que yo no soy impío: y que no hay quien de tu mano libre.
8 “Da hannuwanka ka ƙera ni, kai ka halicce ni. Yanzu kuma kai za ka juya ka hallaka ni?
Tus manos me formaron, y me hicieron todo al derredor: ¿y hásme de deshacer?
9 Ka tuna cewa ka mulmula ni kamar yumɓu. Yanzu za ka mai da ni in zama ƙura kuma?
Acuérdate ahora que como a lodo me hiciste: ¿y hásme de tornar en polvo?
10 Ba kai ka zuba ni kamar madara ba, na daskare kamar cuku.
¿No me fundiste como leche, y como un queso me cuajaste?
11 Ka rufe ni da tsoka da fata, ka harhaɗa ni da ƙasusuwa da jijiyoyi?
Vestísteme de piel y carne, y cubrísteme de huesos y nervios.
12 Ka ba ni rai ka kuma yi mini alheri, kuma cikin tanadinka ka kula da ruhuna.
Vida y misericordia hiciste conmigo; y tu visitación guardó mi espíritu.
13 “Amma wannan shi ne abin da ka ɓoye a zuciyarka, na kuma san abin da yake cikin zuciyarka ke nan.
Y estas cosas tienes guardadas en tu corazón: yo sé que esto está cerca de ti.
14 In na yi zunubi kana kallo na kuma ba za ka fasa ba ni horo ba don laifin da na yi.
Si yo pequé acecharme has tú, y no me limpiarás de mi iniquidad.
15 Idan ina da laifi, kaitona! Ko da ba ni da laifi, ba zan iya ɗaga fuskata ba, gama kunya ta ishe ni duk ɓacin rai ya ishe ni.
Si fuere malo; ¡ay de mí! y si fuere justo, no levantaré mi cabeza, harto de deshonra, y de verme afligido.
16 In na ɗaga kaina, za ka neme ni kamar zaki ka sāke nuna al’ajabin ikonka a kaina.
Y vas creciendo, cazándome como león: tornando, y haciendo en mí maravillas:
17 Kana sāke kawo sababbin waɗanda za su ba da shaida a kaina kana ƙara haushinka a kaina; kana ƙara kawo mini hari.
Renovando tus llagas contra mi, y aumentando conmigo tu furor, remudándose sobre mí ejércitos.
18 “Me ya sa ka fito da ni daga cikin uwata? Da ma na mutu kafin a haife ni.
¿Por qué me sacaste del vientre? Muriera yo, y no me vieran ojos.
19 Da ma ba a halicce ni ba, da na mutu tun daga cikin cikin uwata na wuce zuwa kabari!
Fuera, como si nunca hubiera sido, llevado desde el vientre a la sepultura.
20 ’Yan kwanakina ba su kusa ƙarewa ba ne? Ka rabu da ni don in ɗan samu sukuni na ɗan lokaci
¿Mis días no son una poca cosa? cesa pues, y déjame, para que me esfuerce un poco,
21 kafin in koma inda na fito, ƙasa mai duhu da inuwa sosai,
Antes que vaya, para no volver, a la tierra de tinieblas y de sombra de muerte:
22 zuwa ƙasa mai duhun gaske, da inuwa da hargitsi, inda haske yake kamar duhu.”
Tierra de oscuridad y tenebrosa sombra de muerte, donde no hay orden; y que resplandece como la misma oscuridad.

< Ayuba 10 >