< Ayuba 10 >

1 “Na gaji da rayuwa; saboda haka bari in faɗi zuciyata gabagadi yadda raina yake jin ba daɗi.
A minha alma tem tedio á minha vida: darei livre curso á minha queixa, fallarei na amargura da minha alma.
2 Zan ce wa Allah, kada ka hukunta ni, amma ka gaya mini laifin da na yi maka.
Direi a Deus: Não me condemnes: faze-me saber porque contendes comigo.
3 Kana jin daɗin ba ni wahala, don me ka yashe ni, abin da ka halitta da hannunka, yayinda kake murmushi game da shirye-shiryen mugaye?
Parece-te bem que me opprimas? que rejeites o trabalho das tuas mãos? e resplandeças sobre o conselho dos impios?
4 Idanunka irin na mutum ne? Kana gani yadda mutum yake gani ne?
Tens tu porventura olhos de carne? vês tu como vê o homem?
5 Kwanakinka kamar na mutane ne, ko shekarunka kamar na mutane ne
São os teus dias como os dias do homem? Ou são os teus annos como os annos de um homem,
6 da za ka neme ni da laifi ka hukunta ni?
Para te informares da minha iniquidade, e averiguares o meu peccado?
7 Ko da yake ka san ba ni da laifi, kuma ba wanda zai iya cetona daga hannunka.
Bem sabes tu que eu não sou impio: todavia ninguem ha que me livre da tua mão.
8 “Da hannuwanka ka ƙera ni, kai ka halicce ni. Yanzu kuma kai za ka juya ka hallaka ni?
As tuas mãos me fizeram e me formaram todo em roda; comtudo me consomes.
9 Ka tuna cewa ka mulmula ni kamar yumɓu. Yanzu za ka mai da ni in zama ƙura kuma?
Peço-te que te lembres de que como barro me formaste e me farás tornar em pó.
10 Ba kai ka zuba ni kamar madara ba, na daskare kamar cuku.
Porventura não me vasaste como leite, e como queijo me não coalhaste?
11 Ka rufe ni da tsoka da fata, ka harhaɗa ni da ƙasusuwa da jijiyoyi?
De pelle e carne me vestiste, e com ossos e nervos me ligaste.
12 Ka ba ni rai ka kuma yi mini alheri, kuma cikin tanadinka ka kula da ruhuna.
Vida e beneficencia me fizeste: e o teu cuidado guardou o meu espirito.
13 “Amma wannan shi ne abin da ka ɓoye a zuciyarka, na kuma san abin da yake cikin zuciyarka ke nan.
Porém estas coisas as occultaste no teu coração: bem sei eu que isto esteve comtigo.
14 In na yi zunubi kana kallo na kuma ba za ka fasa ba ni horo ba don laifin da na yi.
Se eu peccar, tu me observas; e da minha iniquidade não me escusarás.
15 Idan ina da laifi, kaitona! Ko da ba ni da laifi, ba zan iya ɗaga fuskata ba, gama kunya ta ishe ni duk ɓacin rai ya ishe ni.
Se fôr impio, ai de mim! e se fôr justo, não levantarei a minha cabeça: farto estou de affronta; e olho para a minha miseria.
16 In na ɗaga kaina, za ka neme ni kamar zaki ka sāke nuna al’ajabin ikonka a kaina.
Porque se vae crescendo; tu me caças como a um leão feroz: tornas-te, e fazes maravilhas contra mim.
17 Kana sāke kawo sababbin waɗanda za su ba da shaida a kaina kana ƙara haushinka a kaina; kana ƙara kawo mini hari.
Tu renovas contra mim as tuas testemunhas, e multiplicas contra mim a tua ira; revezes e combate estão comigo.
18 “Me ya sa ka fito da ni daga cikin uwata? Da ma na mutu kafin a haife ni.
Por quepois me tiraste da madre? Ah se então dera o espirito, e olhos nenhuns me vissem!
19 Da ma ba a halicce ni ba, da na mutu tun daga cikin cikin uwata na wuce zuwa kabari!
Que tivera sido como se nunca fôra: e desde o ventre fôra levado á sepultura!
20 ’Yan kwanakina ba su kusa ƙarewa ba ne? Ka rabu da ni don in ɗan samu sukuni na ɗan lokaci
Porventura não são poucos os meus dias? cessa pois, e deixa-me, para que por um pouco eu tome alento;
21 kafin in koma inda na fito, ƙasa mai duhu da inuwa sosai,
Antes que vá e d'onde nunca torne, á terra da escuridão e da sombra da morte;
22 zuwa ƙasa mai duhun gaske, da inuwa da hargitsi, inda haske yake kamar duhu.”
Terra escurissima, como a mesma escuridão, terra da sombra, da morte e sem ordem alguma e onde a luz é como a escuridão.

< Ayuba 10 >