< Ayuba 10 >

1 “Na gaji da rayuwa; saboda haka bari in faɗi zuciyata gabagadi yadda raina yake jin ba daɗi.
Min sjel er lei av mitt liv, jeg vil la min klage ha fritt løp, jeg vil tale i min sjels bitre smerte.
2 Zan ce wa Allah, kada ka hukunta ni, amma ka gaya mini laifin da na yi maka.
Jeg vil si til Gud: Fordøm mig ikke, la mig vite hvorfor du strider mot mig!
3 Kana jin daɗin ba ni wahala, don me ka yashe ni, abin da ka halitta da hannunka, yayinda kake murmushi game da shirye-shiryen mugaye?
Tykkes det dig godt at du undertrykker, at du forkaster det dine hender med omhu har dannet, og lar ditt lys skinne over ugudeliges råd?
4 Idanunka irin na mutum ne? Kana gani yadda mutum yake gani ne?
Har du menneskeøine, eller ser du således som et menneske ser?
5 Kwanakinka kamar na mutane ne, ko shekarunka kamar na mutane ne
Er dine dager som et menneskes dager, eller dine år som en manns dager? -
6 da za ka neme ni da laifi ka hukunta ni?
siden du søker efter min misgjerning og leter efter min synd,
7 Ko da yake ka san ba ni da laifi, kuma ba wanda zai iya cetona daga hannunka.
enda du vet at jeg ikke er ugudelig, og at det ingen er som redder av din hånd.
8 “Da hannuwanka ka ƙera ni, kai ka halicce ni. Yanzu kuma kai za ka juya ka hallaka ni?
Dine hender har dannet mig og gjort mig, helt og i alle deler, og nu vil du ødelegge mig!
9 Ka tuna cewa ka mulmula ni kamar yumɓu. Yanzu za ka mai da ni in zama ƙura kuma?
Kom i hu at du har dannet mig som leret, og nu lar du mig atter vende tilbake til støvet!
10 Ba kai ka zuba ni kamar madara ba, na daskare kamar cuku.
Helte du mig ikke ut som melk og lot mig størkne som ost?
11 Ka rufe ni da tsoka da fata, ka harhaɗa ni da ƙasusuwa da jijiyoyi?
Med hud og kjøtt klædde du mig, og med ben og sener gjennemvevde du mig.
12 Ka ba ni rai ka kuma yi mini alheri, kuma cikin tanadinka ka kula da ruhuna.
Liv og miskunnhet har du gitt mig, og din varetekt har vernet om min ånd.
13 “Amma wannan shi ne abin da ka ɓoye a zuciyarka, na kuma san abin da yake cikin zuciyarka ke nan.
Og dette gjemte du i ditt hjerte, jeg vet at dette hadde du i sinne:
14 In na yi zunubi kana kallo na kuma ba za ka fasa ba ni horo ba don laifin da na yi.
Syndet jeg, så vilde du vokte på mig og ikke frikjenne mig for min misgjerning;
15 Idan ina da laifi, kaitona! Ko da ba ni da laifi, ba zan iya ɗaga fuskata ba, gama kunya ta ishe ni duk ɓacin rai ya ishe ni.
var jeg skyldig, da ve mig, men var jeg uskyldig, skulde jeg dog ikke kunne løfte mitt hode, mett av skam og med min elendighet for øie;
16 In na ɗaga kaina, za ka neme ni kamar zaki ka sāke nuna al’ajabin ikonka a kaina.
og hevet det sig dog, så vilde du jage efter mig som en løve, og atter vise dig forunderlig mot mig;
17 Kana sāke kawo sababbin waɗanda za su ba da shaida a kaina kana ƙara haushinka a kaina; kana ƙara kawo mini hari.
du vilde føre nye vidner mot mig og øke din harme mot mig, sende alltid nye hærflokker mot mig.
18 “Me ya sa ka fito da ni daga cikin uwata? Da ma na mutu kafin a haife ni.
Hvorfor lot du mig utgå av mors liv? Jeg skulde ha opgitt ånden, og intet øie skulde ha sett mig;
19 Da ma ba a halicce ni ba, da na mutu tun daga cikin cikin uwata na wuce zuwa kabari!
jeg skulde ha vært som om jeg aldri hadde vært til; fra mors liv skulde jeg ha vært båret til graven.
20 ’Yan kwanakina ba su kusa ƙarewa ba ne? Ka rabu da ni don in ɗan samu sukuni na ɗan lokaci
Er ikke mine dager få? - Han holde op! Han la mig være, så jeg kan bli litt glad,
21 kafin in koma inda na fito, ƙasa mai duhu da inuwa sosai,
før jeg går bort for ikke å vende tilbake, bort til mørkets og dødsskyggens land,
22 zuwa ƙasa mai duhun gaske, da inuwa da hargitsi, inda haske yake kamar duhu.”
et land så mørkt som den sorteste natt, hvor dødsskygge og forvirring råder, og hvor lyset er som den sorteste natt!

< Ayuba 10 >