< Ayuba 10 >

1 “Na gaji da rayuwa; saboda haka bari in faɗi zuciyata gabagadi yadda raina yake jin ba daɗi.
[Tædet animam meam vitæ meæ; dimittam adversum me eloquium meum: loquar in amaritudine animæ meæ.
2 Zan ce wa Allah, kada ka hukunta ni, amma ka gaya mini laifin da na yi maka.
Dicam Deo: Noli me condemnare; indica mihi cur me ita judices.
3 Kana jin daɗin ba ni wahala, don me ka yashe ni, abin da ka halitta da hannunka, yayinda kake murmushi game da shirye-shiryen mugaye?
Numquid bonum tibi videtur, si calumnieris me, et opprimas me opus manuum tuarum, et consilium impiorum adjuves?
4 Idanunka irin na mutum ne? Kana gani yadda mutum yake gani ne?
Numquid oculi carnei tibi sunt? aut sicut videt homo, et tu videbis?
5 Kwanakinka kamar na mutane ne, ko shekarunka kamar na mutane ne
Numquid sicut dies hominis dies tui, et anni tui sicut humana sunt tempora,
6 da za ka neme ni da laifi ka hukunta ni?
ut quæras iniquitatem meam, et peccatum meum scruteris,
7 Ko da yake ka san ba ni da laifi, kuma ba wanda zai iya cetona daga hannunka.
et scias quia nihil impium fecerim, cum sit nemo qui de manu tua possit eruere?
8 “Da hannuwanka ka ƙera ni, kai ka halicce ni. Yanzu kuma kai za ka juya ka hallaka ni?
Manus tuæ fecerunt me, et plasmaverunt me totum in circuitu: et sic repente præcipitas me?
9 Ka tuna cewa ka mulmula ni kamar yumɓu. Yanzu za ka mai da ni in zama ƙura kuma?
Memento, quæso, quod sicut lutum feceris me, et in pulverem reduces me.
10 Ba kai ka zuba ni kamar madara ba, na daskare kamar cuku.
Nonne sicut lac mulsisti me, et sicut caseum me coagulasti?
11 Ka rufe ni da tsoka da fata, ka harhaɗa ni da ƙasusuwa da jijiyoyi?
Pelle et carnibus vestisti me; ossibus et nervis compegisti me.
12 Ka ba ni rai ka kuma yi mini alheri, kuma cikin tanadinka ka kula da ruhuna.
Vitam et misericordiam tribuisti mihi, et visitatio tua custodivit spiritum meum.
13 “Amma wannan shi ne abin da ka ɓoye a zuciyarka, na kuma san abin da yake cikin zuciyarka ke nan.
Licet hæc celes in corde tuo, tamen scio quia universorum memineris.
14 In na yi zunubi kana kallo na kuma ba za ka fasa ba ni horo ba don laifin da na yi.
Si peccavi, et ad horam pepercisti mihi, cur ab iniquitate mea mundum me esse non pateris?
15 Idan ina da laifi, kaitona! Ko da ba ni da laifi, ba zan iya ɗaga fuskata ba, gama kunya ta ishe ni duk ɓacin rai ya ishe ni.
Et si impius fuero, væ mihi est; et si justus, non levabo caput, saturatus afflictione et miseria.
16 In na ɗaga kaina, za ka neme ni kamar zaki ka sāke nuna al’ajabin ikonka a kaina.
Et propter superbiam quasi leænam capies me, reversusque mirabiliter me crucias.
17 Kana sāke kawo sababbin waɗanda za su ba da shaida a kaina kana ƙara haushinka a kaina; kana ƙara kawo mini hari.
Instauras testes tuos contra me, et multiplicas iram tuam adversum me, et pœnæ militant in me.
18 “Me ya sa ka fito da ni daga cikin uwata? Da ma na mutu kafin a haife ni.
Quare de vulva eduxisti me? qui utinam consumptus essem, ne oculus me videret.
19 Da ma ba a halicce ni ba, da na mutu tun daga cikin cikin uwata na wuce zuwa kabari!
Fuissem quasi non essem, de utero translatus ad tumulum.
20 ’Yan kwanakina ba su kusa ƙarewa ba ne? Ka rabu da ni don in ɗan samu sukuni na ɗan lokaci
Numquid non paucitas dierum meorum finietur brevi? dimitte ergo me, ut plangam paululum dolorem meum,
21 kafin in koma inda na fito, ƙasa mai duhu da inuwa sosai,
antequam vadam, et non revertar, ad terram tenebrosam, et opertam mortis caligine:
22 zuwa ƙasa mai duhun gaske, da inuwa da hargitsi, inda haske yake kamar duhu.”
terram miseriæ et tenebrarum, ubi umbra mortis et nullus ordo, sed sempiternus horror inhabitat.]

< Ayuba 10 >