< Ayuba 10 >

1 “Na gaji da rayuwa; saboda haka bari in faɗi zuciyata gabagadi yadda raina yake jin ba daɗi.
It loathes self my life my I will let loose on myself complaint my I will speak in [the] bitterness of being my.
2 Zan ce wa Allah, kada ka hukunta ni, amma ka gaya mini laifin da na yi maka.
I will say to God may not you condemn as guilty me make known to me concerning what? do you contend with me.
3 Kana jin daɗin ba ni wahala, don me ka yashe ni, abin da ka halitta da hannunka, yayinda kake murmushi game da shirye-shiryen mugaye?
¿ [is it] good To you - that you will oppress that you will reject [the] product of hands your and on [the] plan of wicked [people] you have shone forth.
4 Idanunka irin na mutum ne? Kana gani yadda mutum yake gani ne?
¿ [do] eyes of Flesh [belong] to you or? as sees a person do you see.
5 Kwanakinka kamar na mutane ne, ko shekarunka kamar na mutane ne
¿ Like [the] days of a person [are] days your or? [are] years your like [the] days of a man.
6 da za ka neme ni da laifi ka hukunta ni?
That you will seek for iniquity my and for sin my you will search.
7 Ko da yake ka san ba ni da laifi, kuma ba wanda zai iya cetona daga hannunka.
On knowledge your that not I am guilty and there not from hand your [is] a deliverer.
8 “Da hannuwanka ka ƙera ni, kai ka halicce ni. Yanzu kuma kai za ka juya ka hallaka ni?
Hands your they formed me and they made me together all around and you have swallowed me.
9 Ka tuna cewa ka mulmula ni kamar yumɓu. Yanzu za ka mai da ni in zama ƙura kuma?
Remember please that like clay you made me and to dust will you turn back? me.
10 Ba kai ka zuba ni kamar madara ba, na daskare kamar cuku.
¿ Not like milk did you pour out me and like cheese did you curdle? me.
11 Ka rufe ni da tsoka da fata, ka harhaɗa ni da ƙasusuwa da jijiyoyi?
Skin and flesh did you clothe? me and with bones and sinews did you weave together? me.
12 Ka ba ni rai ka kuma yi mini alheri, kuma cikin tanadinka ka kula da ruhuna.
Life and loyalty you have done with me and care your it has kept spirit my.
13 “Amma wannan shi ne abin da ka ɓoye a zuciyarka, na kuma san abin da yake cikin zuciyarka ke nan.
And these [things] you hid in heart your I know that this [was] with you.
14 In na yi zunubi kana kallo na kuma ba za ka fasa ba ni horo ba don laifin da na yi.
If I sinned and you will watch me and from iniquity my not you will acquit me.
15 Idan ina da laifi, kaitona! Ko da ba ni da laifi, ba zan iya ɗaga fuskata ba, gama kunya ta ishe ni duk ɓacin rai ya ishe ni.
If I am guilty woe! to me and I have been righteous not I will lift up head my surfeited of shame and see affliction my.
16 In na ɗaga kaina, za ka neme ni kamar zaki ka sāke nuna al’ajabin ikonka a kaina.
So it may rise up like lion you hunt me and you return you show yourself wonderful on me.
17 Kana sāke kawo sababbin waɗanda za su ba da shaida a kaina kana ƙara haushinka a kaina; kana ƙara kawo mini hari.
You renew witnesses your - before me and you increase vexation your with me changes and an army [are] with me.
18 “Me ya sa ka fito da ni daga cikin uwata? Da ma na mutu kafin a haife ni.
And why? from [the] womb did you bring out me I expired and an eye not it saw me.
19 Da ma ba a halicce ni ba, da na mutu tun daga cikin cikin uwata na wuce zuwa kabari!
Just as not I had been I was from [the] womb to the grave I was brought.
20 ’Yan kwanakina ba su kusa ƙarewa ba ne? Ka rabu da ni don in ɗan samu sukuni na ɗan lokaci
¿ Not few [are] days my (and cease and put *Q(K)*) from me so I may be cheerful a little.
21 kafin in koma inda na fito, ƙasa mai duhu da inuwa sosai,
Before I will go and not I will return to [the] land of darkness and deep darkness.
22 zuwa ƙasa mai duhun gaske, da inuwa da hargitsi, inda haske yake kamar duhu.”
[the] land of Darkness - like gloom of deep darkness and not order and it shone forth like gloom.

< Ayuba 10 >