< Ayuba 10 >

1 “Na gaji da rayuwa; saboda haka bari in faɗi zuciyata gabagadi yadda raina yake jin ba daɗi.
I am weary of my life; I will let loose within me my complaint; I will speak in the bitterness of my soul.
2 Zan ce wa Allah, kada ka hukunta ni, amma ka gaya mini laifin da na yi maka.
I will say unto God, Do not condemn me! Show me wherefore thou contendest with me!
3 Kana jin daɗin ba ni wahala, don me ka yashe ni, abin da ka halitta da hannunka, yayinda kake murmushi game da shirye-shiryen mugaye?
Is it a pleasure to thee to oppress, And to despise the work of thy hands, And to shine upon the plans of the wicked?
4 Idanunka irin na mutum ne? Kana gani yadda mutum yake gani ne?
Hast thou eyes of flesh, Or seest thou as man seeth?
5 Kwanakinka kamar na mutane ne, ko shekarunka kamar na mutane ne
Are thy days as the days of a man, Are thy years as the days of a mortal,
6 da za ka neme ni da laifi ka hukunta ni?
That thou seekest after my iniquity, And searchest after my sin,
7 Ko da yake ka san ba ni da laifi, kuma ba wanda zai iya cetona daga hannunka.
Though thou knowest that I am not guilty, And that none can deliver from thy hand?
8 “Da hannuwanka ka ƙera ni, kai ka halicce ni. Yanzu kuma kai za ka juya ka hallaka ni?
Have thy hands completely fashioned and made me In every part, that thou mightst destroy me?
9 Ka tuna cewa ka mulmula ni kamar yumɓu. Yanzu za ka mai da ni in zama ƙura kuma?
O remember that thou hast moulded me as clay! And wilt thou bring me again to dust?
10 Ba kai ka zuba ni kamar madara ba, na daskare kamar cuku.
Thou didst pour me out as milk, And curdle me as cheese;
11 Ka rufe ni da tsoka da fata, ka harhaɗa ni da ƙasusuwa da jijiyoyi?
With skin and flesh didst thou clothe me, And strengthen me with bones and sinews;
12 Ka ba ni rai ka kuma yi mini alheri, kuma cikin tanadinka ka kula da ruhuna.
Thou didst grant me life and favor, And thy protection preserved my breath:
13 “Amma wannan shi ne abin da ka ɓoye a zuciyarka, na kuma san abin da yake cikin zuciyarka ke nan.
Yet these things thou didst lay up in thy heart! I know that this was in thy mind.
14 In na yi zunubi kana kallo na kuma ba za ka fasa ba ni horo ba don laifin da na yi.
If I sin, then thou markest me, And wilt not acquit me of mine iniquity.
15 Idan ina da laifi, kaitona! Ko da ba ni da laifi, ba zan iya ɗaga fuskata ba, gama kunya ta ishe ni duk ɓacin rai ya ishe ni.
If I am wicked, —then woe unto me! Yet if righteous, I dare not lift up my head; I am full of confusion, beholding my affliction.
16 In na ɗaga kaina, za ka neme ni kamar zaki ka sāke nuna al’ajabin ikonka a kaina.
If I lift it up, like a lion thou huntest me, And again showest thyself terrible unto me.
17 Kana sāke kawo sababbin waɗanda za su ba da shaida a kaina kana ƙara haushinka a kaina; kana ƙara kawo mini hari.
Thou renewest thy witnesses against me, And increasest thine anger toward me; New hosts continually rise up against me.
18 “Me ya sa ka fito da ni daga cikin uwata? Da ma na mutu kafin a haife ni.
Why then didst thou bring me forth from the womb? I should have perished, and no eye had seen me;
19 Da ma ba a halicce ni ba, da na mutu tun daga cikin cikin uwata na wuce zuwa kabari!
I should be as though I had not been; I should have been borne from the womb to the grave.
20 ’Yan kwanakina ba su kusa ƙarewa ba ne? Ka rabu da ni don in ɗan samu sukuni na ɗan lokaci
Are not my days few? O spare then, And let me alone, that I may be at ease a little while,
21 kafin in koma inda na fito, ƙasa mai duhu da inuwa sosai,
Before I go— whence I shall not return—To the land of darkness and death-shade,
22 zuwa ƙasa mai duhun gaske, da inuwa da hargitsi, inda haske yake kamar duhu.”
The land of darkness like the blackness of death-shade, Where is no order, and where the light is as darkness.

< Ayuba 10 >