< Ayuba 10 >

1 “Na gaji da rayuwa; saboda haka bari in faɗi zuciyata gabagadi yadda raina yake jin ba daɗi.
"My soul is weary of my life. I will give free course to my complaint. I will speak in the bitterness of my soul.
2 Zan ce wa Allah, kada ka hukunta ni, amma ka gaya mini laifin da na yi maka.
I will tell God, 'Do not condemn me. Show me why you contend with me.
3 Kana jin daɗin ba ni wahala, don me ka yashe ni, abin da ka halitta da hannunka, yayinda kake murmushi game da shirye-shiryen mugaye?
Is it good to you that you should oppress, that you should despise the work of your hands, and smile on the counsel of the wicked?
4 Idanunka irin na mutum ne? Kana gani yadda mutum yake gani ne?
Do you have eyes of flesh? Or do you see as man sees?
5 Kwanakinka kamar na mutane ne, ko shekarunka kamar na mutane ne
Are your days as the days of mortals, or your years as man's years,
6 da za ka neme ni da laifi ka hukunta ni?
that you inquire after my iniquity, and search after my sin?
7 Ko da yake ka san ba ni da laifi, kuma ba wanda zai iya cetona daga hannunka.
Although you know that I am not wicked, there is no one who can deliver out of your hand.
8 “Da hannuwanka ka ƙera ni, kai ka halicce ni. Yanzu kuma kai za ka juya ka hallaka ni?
"'Your hands have framed me and fashioned me altogether, yet you destroy me.
9 Ka tuna cewa ka mulmula ni kamar yumɓu. Yanzu za ka mai da ni in zama ƙura kuma?
Remember, I beg you, that you have fashioned me as clay. Will you bring me into dust again?
10 Ba kai ka zuba ni kamar madara ba, na daskare kamar cuku.
Haven't you poured me out like milk, and curdled me like cheese?
11 Ka rufe ni da tsoka da fata, ka harhaɗa ni da ƙasusuwa da jijiyoyi?
You have clothed me with skin and flesh, and knit me together with bones and sinews.
12 Ka ba ni rai ka kuma yi mini alheri, kuma cikin tanadinka ka kula da ruhuna.
You have granted me life and loving kindness. Your visitation has preserved my spirit.
13 “Amma wannan shi ne abin da ka ɓoye a zuciyarka, na kuma san abin da yake cikin zuciyarka ke nan.
Yet you hid these things in your heart. I know that this is with you:
14 In na yi zunubi kana kallo na kuma ba za ka fasa ba ni horo ba don laifin da na yi.
if I sin, then you mark me. You will not acquit me from my iniquity.
15 Idan ina da laifi, kaitona! Ko da ba ni da laifi, ba zan iya ɗaga fuskata ba, gama kunya ta ishe ni duk ɓacin rai ya ishe ni.
If I am wicked, woe to me. If I am righteous, I still shall not lift up my head, being filled with disgrace, and conscious of my affliction.
16 In na ɗaga kaina, za ka neme ni kamar zaki ka sāke nuna al’ajabin ikonka a kaina.
And if I lift myself up, you hunt me like a lion. Again you show yourself powerful to me.
17 Kana sāke kawo sababbin waɗanda za su ba da shaida a kaina kana ƙara haushinka a kaina; kana ƙara kawo mini hari.
You renew your witnesses against me, and increase your indignation on me. Changes and warfare are with me.
18 “Me ya sa ka fito da ni daga cikin uwata? Da ma na mutu kafin a haife ni.
"'Why, then, have you brought me forth out of the womb? I wish I had given up the spirit, and no eye had seen me.
19 Da ma ba a halicce ni ba, da na mutu tun daga cikin cikin uwata na wuce zuwa kabari!
I should have been as though I had not been. I should have been carried from the womb to the grave.
20 ’Yan kwanakina ba su kusa ƙarewa ba ne? Ka rabu da ni don in ɗan samu sukuni na ɗan lokaci
Aren't my days few? Cease then. Leave me alone, that I may find a little comfort,
21 kafin in koma inda na fito, ƙasa mai duhu da inuwa sosai,
before I go where I shall not return from, to the land of darkness and of the shadow of death;
22 zuwa ƙasa mai duhun gaske, da inuwa da hargitsi, inda haske yake kamar duhu.”
the land dark as midnight, of the shadow of death, without any order, where the light is as midnight.'"

< Ayuba 10 >