< Ayuba 10 >
1 “Na gaji da rayuwa; saboda haka bari in faɗi zuciyata gabagadi yadda raina yake jin ba daɗi.
Weary in my soul, I will pour my words with groans upon him: I will speak being straitened in the bitterness of my soul.
2 Zan ce wa Allah, kada ka hukunta ni, amma ka gaya mini laifin da na yi maka.
And I will say to the Lord, Do not teach me to be impious; and wherefore hast thou thus judged me?
3 Kana jin daɗin ba ni wahala, don me ka yashe ni, abin da ka halitta da hannunka, yayinda kake murmushi game da shirye-shiryen mugaye?
Is it good before thee if I be unrighteous? for thou hast disowned the work of thy hands, and attended to the counsel of the ungodly.
4 Idanunka irin na mutum ne? Kana gani yadda mutum yake gani ne?
Or dost thou see as a mortal sees? or wilt thou look as a man sees?
5 Kwanakinka kamar na mutane ne, ko shekarunka kamar na mutane ne
Or is thy life human, or thy years [the years] of a man,
6 da za ka neme ni da laifi ka hukunta ni?
that thou hast enquired into mine iniquity, and searched out my sins?
7 Ko da yake ka san ba ni da laifi, kuma ba wanda zai iya cetona daga hannunka.
For thou knowest that I have not committed iniquity: but who is he that can deliver out of thy hands?
8 “Da hannuwanka ka ƙera ni, kai ka halicce ni. Yanzu kuma kai za ka juya ka hallaka ni?
Thy hands have formed me and made me; afterwards thou didst change [thy mind], and smite me.
9 Ka tuna cewa ka mulmula ni kamar yumɓu. Yanzu za ka mai da ni in zama ƙura kuma?
Remember that thou hast made me [as] clay, and thou dost turn me again to earth.
10 Ba kai ka zuba ni kamar madara ba, na daskare kamar cuku.
Hast thou not poured me out like milk, and curdled me like cheese?
11 Ka rufe ni da tsoka da fata, ka harhaɗa ni da ƙasusuwa da jijiyoyi?
And thou didst clothe me with skin and flesh, and frame me with bones and sinews.
12 Ka ba ni rai ka kuma yi mini alheri, kuma cikin tanadinka ka kula da ruhuna.
And thou didst bestow upon me life and mercy, and thy oversight has preserved my spirit.
13 “Amma wannan shi ne abin da ka ɓoye a zuciyarka, na kuma san abin da yake cikin zuciyarka ke nan.
Having these things in thyself, I know that thou canst do all things; for nothing is impossible with thee.
14 In na yi zunubi kana kallo na kuma ba za ka fasa ba ni horo ba don laifin da na yi.
And if I should sin, thou watchest me; and thou hast not cleared me from iniquity.
15 Idan ina da laifi, kaitona! Ko da ba ni da laifi, ba zan iya ɗaga fuskata ba, gama kunya ta ishe ni duk ɓacin rai ya ishe ni.
Or if I should be ungodly, woe is me: and if I should be righteous, I cannot lift myself up, for I am full of dishonour.
16 In na ɗaga kaina, za ka neme ni kamar zaki ka sāke nuna al’ajabin ikonka a kaina.
For I am hunted like a lion for slaughter; for again thou hast changed and art terribly destroying me;
17 Kana sāke kawo sababbin waɗanda za su ba da shaida a kaina kana ƙara haushinka a kaina; kana ƙara kawo mini hari.
renewing against me my torture: and thou hast dealt with me in great anger, and thou hast brought trials upon me.
18 “Me ya sa ka fito da ni daga cikin uwata? Da ma na mutu kafin a haife ni.
Why then didst thou bring me out of the womb? and why did I not die, and no eye see me,
19 Da ma ba a halicce ni ba, da na mutu tun daga cikin cikin uwata na wuce zuwa kabari!
and I become as if I had not been? for why was I not carried from the womb to the grave?
20 ’Yan kwanakina ba su kusa ƙarewa ba ne? Ka rabu da ni don in ɗan samu sukuni na ɗan lokaci
Is not the time of my life short? suffer me to rest a little,
21 kafin in koma inda na fito, ƙasa mai duhu da inuwa sosai,
before I go whence I shall not return, to a land of darkness and gloominess;
22 zuwa ƙasa mai duhun gaske, da inuwa da hargitsi, inda haske yake kamar duhu.”
to a land of perpetual darkness, where there is no light, neither [can any one] see the life of mortals.