< Ayuba 10 >

1 “Na gaji da rayuwa; saboda haka bari in faɗi zuciyata gabagadi yadda raina yake jin ba daɗi.
My soul is tired of life; I will let my sad thoughts go free in words; my soul will make a bitter outcry.
2 Zan ce wa Allah, kada ka hukunta ni, amma ka gaya mini laifin da na yi maka.
I will say to God, Do not put me down as a sinner; make clear to me what you have against me.
3 Kana jin daɗin ba ni wahala, don me ka yashe ni, abin da ka halitta da hannunka, yayinda kake murmushi game da shirye-shiryen mugaye?
What profit is it to you to be cruel, to give up the work of your hands, looking kindly on the design of evil-doers?
4 Idanunka irin na mutum ne? Kana gani yadda mutum yake gani ne?
Have you eyes of flesh, or do you see as man sees?
5 Kwanakinka kamar na mutane ne, ko shekarunka kamar na mutane ne
Are your days as the days of man, or your years like his,
6 da za ka neme ni da laifi ka hukunta ni?
That you take note of my sin, searching after my wrongdoing,
7 Ko da yake ka san ba ni da laifi, kuma ba wanda zai iya cetona daga hannunka.
Though you see that I am not an evil-doer; and there is no one who is able to take a man out of your hands?
8 “Da hannuwanka ka ƙera ni, kai ka halicce ni. Yanzu kuma kai za ka juya ka hallaka ni?
Your hands made me, and I was formed by you, but then, changing your purpose, you gave me up to destruction.
9 Ka tuna cewa ka mulmula ni kamar yumɓu. Yanzu za ka mai da ni in zama ƙura kuma?
O keep in mind that you made me out of earth; and will you send me back again to dust?
10 Ba kai ka zuba ni kamar madara ba, na daskare kamar cuku.
Was I not drained out like milk, becoming hard like cheese?
11 Ka rufe ni da tsoka da fata, ka harhaɗa ni da ƙasusuwa da jijiyoyi?
By you I was clothed with skin and flesh, and joined together with bones and muscles.
12 Ka ba ni rai ka kuma yi mini alheri, kuma cikin tanadinka ka kula da ruhuna.
You have been kind to me, and your grace has been with me, and your care has kept my spirit safe.
13 “Amma wannan shi ne abin da ka ɓoye a zuciyarka, na kuma san abin da yake cikin zuciyarka ke nan.
But you kept these things in the secret of your heart; I am certain this was in your thoughts:
14 In na yi zunubi kana kallo na kuma ba za ka fasa ba ni horo ba don laifin da na yi.
That, if I did wrong, you would take note of it, and would not make me clear from sin:
15 Idan ina da laifi, kaitona! Ko da ba ni da laifi, ba zan iya ɗaga fuskata ba, gama kunya ta ishe ni duk ɓacin rai ya ishe ni.
That, if I was an evil-doer, the curse would come on me; and if I was upright, my head would not be lifted up, being full of shame and overcome with trouble.
16 In na ɗaga kaina, za ka neme ni kamar zaki ka sāke nuna al’ajabin ikonka a kaina.
And that if there was cause for pride, you would go after me like a lion; and again put out your wonders against me:
17 Kana sāke kawo sababbin waɗanda za su ba da shaida a kaina kana ƙara haushinka a kaina; kana ƙara kawo mini hari.
That you would send new witnesses against me, increasing your wrath against me, and letting loose new armies on me.
18 “Me ya sa ka fito da ni daga cikin uwata? Da ma na mutu kafin a haife ni.
Why then did you make me come out of my mother's body? It would have been better for me to have taken my last breath, and for no eye to have seen me,
19 Da ma ba a halicce ni ba, da na mutu tun daga cikin cikin uwata na wuce zuwa kabari!
And for me to have been as if I had not been; to have been taken from my mother's body straight to my last resting-place.
20 ’Yan kwanakina ba su kusa ƙarewa ba ne? Ka rabu da ni don in ɗan samu sukuni na ɗan lokaci
Are not the days of my life small in number? Let your eyes be turned away from me, so that I may have a little pleasure,
21 kafin in koma inda na fito, ƙasa mai duhu da inuwa sosai,
Before I go to the place from which I will not come back, to the land where all is dark and black,
22 zuwa ƙasa mai duhun gaske, da inuwa da hargitsi, inda haske yake kamar duhu.”
A land of thick dark, without order, where the very light is dark.

< Ayuba 10 >