< Ayuba 1 >
1 A ƙasar Uz akwai wani mutum mai suna Ayuba. Mutum ne marar laifi kuma mai adalci; yana tsoron Allah, ba ruwansa da mugunta.
Человек некий бяше во стране Авситидийстей, емуже имя Иов, и бе человек он истинен, непорочен, праведен богочестив, удаляяся от всякия лукавыя вещи.
2 Yana da’ya’ya maza bakwai da’yan mata uku,
Быша же ему сынове седмь и дщери три.
3 yana da tumaki dubu bakwai, raƙuma dubu uku, shanu ɗari biyar, da jakuna ɗari biyar, yana kuma da masu yi masa aiki da yawa. A ƙasar Gabas ba wani kamar sa.
И бяху скоти его, овец седмь тысящ, велблюдов три тысящы, супруг волов пять сот, и ослиц пасомых пять сот, и слуг много зело, и дела велия бяху ему на земли: и бе человек оный благороднейший сущих от Восток солнца.
4 ’Ya’yansa maza sukan yi biki a gidajensu, wannan yă yi yă ba wancan, sai su kira’yan’uwansu mata ukun su ci, su sha tare.
Сходящеся же сынове его друг ко другу, творяху пир на кийждо день, споемлюще вкупе и три сестры своя, ясти и пити с ними.
5 Bayan lokacin bikin ya wuce, sai Ayuba yă aika su zo don yă tsarkake su. Tun da sassafe zai miƙa hadaya ta ƙonawa domin kowannensu, don yana tunani cewa, “Mai yiwuwa’ya’yana sun yi wa Allah zunubi, ko sun la’anta shi a cikin zuciyarsu.” Haka Ayuba ya saba yi.
И егда скончавашеся дние пира, посылаше Иов и очищаше их, востая заутра, и приношаше о них жертвы по числу их, и телца единаго о гресе о душах их. Глаголаше бо Иов: негли когда сынове мои согрешиша и в мысли своей злая помыслиша противу Бога? Тако убо творяше Иов вся дни.
6 Wata rana mala’iku suka kawo kansu gaban Ubangiji, Shaiɗan shi ma ya zo tare da su.
И бысть яко день сей, и се, приидоша Ангели Божии предстати пред Господем, и диавол прииде с ними.
7 Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “Daga ina ka fito?” Shaiɗan ya amsa wa Ubangiji ya ce, “Daga yawo a duniya ina kai da kawowa a cikinta.”
И рече Господь диаволу: откуду пришел еси? И отвещав диавол Господеви, рече: обшед землю и прошед поднебесную, се, есмь.
8 Sai Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “Ko ka ga bawana Ayuba? A cikin duniya babu wani kamar sa; shi marar laifi ne, adali kuma, mutum ne mai tsoron Allah, ba ruwansa da mugunta.”
И рече ему Господь: внял ли еси мыслию твоею на раба Моего Иова? Зане несть яко он на земли: человек непорочен, истинен, богочестив, удаляяся от всякия лукавыя вещи.
9 Sai Shaiɗan ya amsa ya ce, “Haka kawai Ayuba yake tsoron Allah?
Отвеща же диавол и рече пред Господем:
10 Ba ka kāre shi da iyalinsa gaba ɗaya da duk mallakarsa ba? Ka Albarkaci ayyukan hannunsa yadda dabbobinsa duk sun cika ko’ina.
еда туне Иов чтит Господа? Не Ты ли оградил еси внешняя его и внутренняя дому его, и яже вне всех сущих его окрест? Дела же руку его благословил еси и скоты его многи сотворил еси на земли:
11 Ka ɗan miƙa hannunka ka raba shi da duk abin da yake da shi, ba shakka zai la’anta ka kana ji, kana gani.”
но посли руку Твою и коснися всех, яже имать, аще не в лице Тя благословит,
12 Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “To, shi ke nan, duk abin da yake da shi yana hannunka, amma kada ka taɓa shi, shi kansa.” Sai Shaiɗan ya bar Ubangiji.
тогда рече Господь диаволу: се, вся, елика суть ему, даю в руку твою, но самого да не коснешися. И изыде диавол от Господа.
13 Wata rana lokacin da’ya’yan Ayuba suke cikin biki a gidan babban ɗansa,
И бысть яко день сей, сынове иовлевы и дщери его пияху вино в дому брата своего старейшаго.
14 sai ɗan aika ya zo wurin Ayuba ya ce masa, “Shanu suna huɗa, jakuna kuma suna kiwo nan kusa,
И се, вестник прииде ко Иову и рече ему: супрузи волов оряху, и ослицы пасяхуся близ их:
15 sai Sabenawa suka auka musu suka kwashe su suka tafi, suka karkashe masu yi maka aiki duka, ni kaɗai na tsira na zo in gaya maka!”
и пришедше пленителие плениша их и отроки избиша мечем, и спасохся аз един и приидох возвестити тебе.
16 Yana cikin magana sai ga wani ɗan aika ya zo ya ce, “Wutar Allah ta sauko daga sama ta ƙona dukan tumaki da masu lura da su, wato, bayinka, ni kaɗai na tsira na zo in gaya maka!”
Еще сему глаголющу, прииде ин вестник и рече ко Иову: огнь спаде с небесе и пожже овцы и пастыри пояде подобне, спасохся же аз един и приидох возвестити тебе.
17 Yana cikin magana sai ga wani ɗan aika ya zo ya ce, “Ƙungiyoyin mahara uku na Kaldiyawa sun auka wa raƙumanka sun kwashe su duka, suka kuma karkashe masu yi maka aiki, ni kaɗai ne na tsira na zo in gaya maka!”
Еще сему глаголющу, прииде ин вестник и рече ко Иову: конницы сотвориша началства три и окружиша велблюды и плениша их и отроки избиша мечьми, спасохся же аз един и приидох возвестити тебе.
18 Yana cikin magana, sai ga wani ɗan aika ya zo ya ce, “’Ya’yanka maza da mata suna biki, suna ci suna sha a gidan babban ɗanka,
Еще сему глаголющу, ин вестник прииде, глаголя Иову: сыном твоим и дщерем твоим ядущым и пиющым у брата своего старейшаго,
19 sai wata iska mai ƙarfi daga hamada ta auka ta rushe gidan, gidan kuwa ya fāɗi a kan’ya’yanka ya kashe su, ni kaɗai na tsira na zo in gaya maka!”
внезапу ветр велик найде от пустыни и коснуся четырем углом храмины, и паде храмина на дети твоя, и скончашася: спасохся же аз един и приидох возвестити тебе.
20 Da jin haka sai Ayuba ya tashi ya yayyaga tufafin jikinsa, ya aske kansa. Ya fāɗi a ƙasa ya yi sujada
Тако (услышав) Иов, востав растерза ризы своя и остриже власы главы своея, (и посыпа перстию главу свою, ) и пад на землю, поклонися (Господеви)
21 ya ce, “Tsirara na fito daga cikin mahaifiyata, tsirara kuma zan koma. Ubangiji ya bayar, Ubangiji kuma ya karɓa; yabo ya tabbata ga Ubangiji.”
и рече: сам наг изыдох от чрева матере моея, наг и отиду тамо: Господь даде, Господь отят: яко Господеви изволися, тако бысть: буди имя Господне благословено (во веки).
22 Cikin wannan duka Ayuba bai yi wa Allah zunubi ta wurin ba shi laifi ba.
Во всех сих приключившихся ему ничтоже согреши Иов пред Господем, (ниже устнама своима, ) и не даде безумия Богу.