< Ayuba 1 >

1 A ƙasar Uz akwai wani mutum mai suna Ayuba. Mutum ne marar laifi kuma mai adalci; yana tsoron Allah, ba ruwansa da mugunta.
Havia um homem na terra de Uz, cujo nome era Job. Esse homem era irrepreensível e íntegro, e um que temia a Deus, e se afastava do mal.
2 Yana da’ya’ya maza bakwai da’yan mata uku,
There nasceram para ele sete filhos e três filhas.
3 yana da tumaki dubu bakwai, raƙuma dubu uku, shanu ɗari biyar, da jakuna ɗari biyar, yana kuma da masu yi masa aiki da yawa. A ƙasar Gabas ba wani kamar sa.
Seus bens também eram sete mil ovelhas, três mil camelos, quinhentas cangas de bois, quinhentas burras e um lar muito grande; de modo que este homem era o maior de todos os filhos do oriente.
4 ’Ya’yansa maza sukan yi biki a gidajensu, wannan yă yi yă ba wancan, sai su kira’yan’uwansu mata ukun su ci, su sha tare.
Seus filhos foram e fizeram uma festa na casa de cada um no seu aniversário; e mandaram e chamaram suas três irmãs para comer e beber com eles.
5 Bayan lokacin bikin ya wuce, sai Ayuba yă aika su zo don yă tsarkake su. Tun da sassafe zai miƙa hadaya ta ƙonawa domin kowannensu, don yana tunani cewa, “Mai yiwuwa’ya’yana sun yi wa Allah zunubi, ko sun la’anta shi a cikin zuciyarsu.” Haka Ayuba ya saba yi.
Foi assim que, quando os dias de sua festa terminaram, Jó os enviou e os santificou, levantando-se de manhã cedo, e ofereceu holocaustos de acordo com o número de todos eles. Pois Jó disse: “Pode ser que meus filhos tenham pecado, e renunciado a Deus em seus corações”. Jó o fez continuamente.
6 Wata rana mala’iku suka kawo kansu gaban Ubangiji, Shaiɗan shi ma ya zo tare da su.
Agora, no dia em que os filhos de Deus vieram se apresentar diante de Javé, Satanás também veio entre eles.
7 Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “Daga ina ka fito?” Shaiɗan ya amsa wa Ubangiji ya ce, “Daga yawo a duniya ina kai da kawowa a cikinta.”
Yahweh disse a Satanás: “De onde você veio?” Então Satanás respondeu a Javé, e disse: “De ir e vir na terra, e de andar para cima e para baixo nela”.
8 Sai Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “Ko ka ga bawana Ayuba? A cikin duniya babu wani kamar sa; shi marar laifi ne, adali kuma, mutum ne mai tsoron Allah, ba ruwansa da mugunta.”
Yahweh disse a Satanás: “Você já considerou meu servo, Jó? Pois não há ninguém como ele na terra, um homem irrepreensível e íntegro, que teme a Deus e se afasta do mal”.
9 Sai Shaiɗan ya amsa ya ce, “Haka kawai Ayuba yake tsoron Allah?
Então Satanás respondeu a Javé e disse: “Será que Jó teme a Deus por nada?
10 Ba ka kāre shi da iyalinsa gaba ɗaya da duk mallakarsa ba? Ka Albarkaci ayyukan hannunsa yadda dabbobinsa duk sun cika ko’ina.
Você não fez uma sebe ao redor dele, e ao redor de sua casa, e ao redor de tudo o que ele tem, de todos os lados? Você tem abençoado o trabalho de suas mãos, e sua substância é aumentada na terra.
11 Ka ɗan miƙa hannunka ka raba shi da duk abin da yake da shi, ba shakka zai la’anta ka kana ji, kana gani.”
Mas estenda sua mão agora, e toque tudo o que ele tem, e ele renunciará a você na sua cara”.
12 Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “To, shi ke nan, duk abin da yake da shi yana hannunka, amma kada ka taɓa shi, shi kansa.” Sai Shaiɗan ya bar Ubangiji.
Yahweh disse a Satanás: “Eis que tudo o que ele tem está em seu poder”. Só sobre si mesmo não estenda sua mão”. Assim, Satanás saiu da presença de Iavé.
13 Wata rana lokacin da’ya’yan Ayuba suke cikin biki a gidan babban ɗansa,
Caiu num dia em que seus filhos e suas filhas estavam comendo e bebendo vinho na casa de seu irmão mais velho,
14 sai ɗan aika ya zo wurin Ayuba ya ce masa, “Shanu suna huɗa, jakuna kuma suna kiwo nan kusa,
que um mensageiro veio a Jó, e disse: “Os bois estavam arando, e os burros alimentando-se ao seu lado,
15 sai Sabenawa suka auka musu suka kwashe su suka tafi, suka karkashe masu yi maka aiki duka, ni kaɗai na tsira na zo in gaya maka!”
e os Sabeanos atacaram, e os levaram embora. Sim, eles mataram os servos com o fio da espada, e eu sozinho escapei para contar a vocês”.
16 Yana cikin magana sai ga wani ɗan aika ya zo ya ce, “Wutar Allah ta sauko daga sama ta ƙona dukan tumaki da masu lura da su, wato, bayinka, ni kaɗai na tsira na zo in gaya maka!”
Enquanto ele ainda estava falando, outro também veio e disse: “O fogo de Deus caiu do céu, e queimou as ovelhas e os servos, e os consumiu, e só eu escapei para lhe dizer”.
17 Yana cikin magana sai ga wani ɗan aika ya zo ya ce, “Ƙungiyoyin mahara uku na Kaldiyawa sun auka wa raƙumanka sun kwashe su duka, suka kuma karkashe masu yi maka aiki, ni kaɗai ne na tsira na zo in gaya maka!”
Enquanto ele ainda estava falando, outro também veio e disse: “Os caldeus fizeram três faixas, e varreram os camelos, e os levaram, sim, e mataram os criados com o fio da espada; e eu sozinho escapei para contar”.
18 Yana cikin magana, sai ga wani ɗan aika ya zo ya ce, “’Ya’yanka maza da mata suna biki, suna ci suna sha a gidan babban ɗanka,
Enquanto ele ainda estava falando, veio também outro, e disse: “Seus filhos e suas filhas estavam comendo e bebendo vinho na casa de seu irmão mais velho,
19 sai wata iska mai ƙarfi daga hamada ta auka ta rushe gidan, gidan kuwa ya fāɗi a kan’ya’yanka ya kashe su, ni kaɗai na tsira na zo in gaya maka!”
e eis que veio um grande vento do deserto, e atingiu os quatro cantos da casa, e caiu sobre os jovens, e eles estão mortos. Só eu escapei para contar a vocês”.
20 Da jin haka sai Ayuba ya tashi ya yayyaga tufafin jikinsa, ya aske kansa. Ya fāɗi a ƙasa ya yi sujada
Então Jó se levantou, rasgou seu manto, rapou sua cabeça, caiu no chão, e adorou.
21 ya ce, “Tsirara na fito daga cikin mahaifiyata, tsirara kuma zan koma. Ubangiji ya bayar, Ubangiji kuma ya karɓa; yabo ya tabbata ga Ubangiji.”
Ele disse: “Saí nu do ventre de minha mãe e, nu, voltarei lá”. Yahweh deu, e Yahweh levou. Bendito seja o nome de Iavé”.
22 Cikin wannan duka Ayuba bai yi wa Allah zunubi ta wurin ba shi laifi ba.
Em tudo isso, Jó não pecou, nem acusou Deus de transgressão.

< Ayuba 1 >