< Ayuba 1 >

1 A ƙasar Uz akwai wani mutum mai suna Ayuba. Mutum ne marar laifi kuma mai adalci; yana tsoron Allah, ba ruwansa da mugunta.
Il y avait au pays d'Uz un homme dont le nom était Job. Cet homme était irréprochable et droit, il craignait Dieu et se détournait du mal.
2 Yana da’ya’ya maza bakwai da’yan mata uku,
Il lui naquit sept fils et trois filles.
3 yana da tumaki dubu bakwai, raƙuma dubu uku, shanu ɗari biyar, da jakuna ɗari biyar, yana kuma da masu yi masa aiki da yawa. A ƙasar Gabas ba wani kamar sa.
Il possédait aussi sept mille moutons, trois mille chameaux, cinq cents paires de bœufs, cinq cents ânes femelles, et une très grande maison, de sorte que cet homme était le plus grand de tous les enfants de l'Orient.
4 ’Ya’yansa maza sukan yi biki a gidajensu, wannan yă yi yă ba wancan, sai su kira’yan’uwansu mata ukun su ci, su sha tare.
Ses fils allèrent faire un festin dans la maison de chacun d'eux le jour de son anniversaire; et ils envoyèrent chercher leurs trois sœurs pour manger et boire avec eux.
5 Bayan lokacin bikin ya wuce, sai Ayuba yă aika su zo don yă tsarkake su. Tun da sassafe zai miƙa hadaya ta ƙonawa domin kowannensu, don yana tunani cewa, “Mai yiwuwa’ya’yana sun yi wa Allah zunubi, ko sun la’anta shi a cikin zuciyarsu.” Haka Ayuba ya saba yi.
Lorsque leurs jours de fête furent écoulés, Job les envoya et les sanctifia; il se leva de bon matin et offrit des holocaustes selon leur nombre. Car Job disait: « Il se peut que mes fils aient péché et renoncé à Dieu dans leur cœur. » Et Job ne cessait de le faire.
6 Wata rana mala’iku suka kawo kansu gaban Ubangiji, Shaiɗan shi ma ya zo tare da su.
Or, le jour où les fils de Dieu vinrent se présenter devant Yahvé, Satan aussi vint au milieu d'eux.
7 Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “Daga ina ka fito?” Shaiɗan ya amsa wa Ubangiji ya ce, “Daga yawo a duniya ina kai da kawowa a cikinta.”
Yahvé dit à Satan: « D'où viens-tu? » Alors Satan répondit à Yahvé: « D'aller et de venir sur la terre, et d'y monter et d'y descendre. »
8 Sai Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “Ko ka ga bawana Ayuba? A cikin duniya babu wani kamar sa; shi marar laifi ne, adali kuma, mutum ne mai tsoron Allah, ba ruwansa da mugunta.”
Yahvé dit à Satan: « As-tu considéré mon serviteur Job? Car il n'y a personne comme lui sur la terre, un homme irréprochable et droit, qui craint Dieu et se détourne du mal. »
9 Sai Shaiɗan ya amsa ya ce, “Haka kawai Ayuba yake tsoron Allah?
Alors Satan prit la parole devant Yahvé, et dit: Job craint-il Dieu pour rien?
10 Ba ka kāre shi da iyalinsa gaba ɗaya da duk mallakarsa ba? Ka Albarkaci ayyukan hannunsa yadda dabbobinsa duk sun cika ko’ina.
N'as-tu pas fait une haie autour de lui, autour de sa maison, et autour de tout ce qu'il possède, de tous côtés? Tu as béni l'ouvrage de ses mains, et ses biens se sont accrus dans le pays.
11 Ka ɗan miƙa hannunka ka raba shi da duk abin da yake da shi, ba shakka zai la’anta ka kana ji, kana gani.”
Mais étends maintenant ta main et touche à tout ce qu'il possède, et il te reniera en face. »
12 Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “To, shi ke nan, duk abin da yake da shi yana hannunka, amma kada ka taɓa shi, shi kansa.” Sai Shaiɗan ya bar Ubangiji.
Yahvé dit à Satan: « Voici, tout ce qu'il possède est en ton pouvoir. Seulement sur lui-même, n'étends pas ta main. » Et Satan sortit de la présence de Yahvé.
13 Wata rana lokacin da’ya’yan Ayuba suke cikin biki a gidan babban ɗansa,
Un jour que ses fils et ses filles mangeaient et buvaient du vin dans la maison de leur frère aîné,
14 sai ɗan aika ya zo wurin Ayuba ya ce masa, “Shanu suna huɗa, jakuna kuma suna kiwo nan kusa,
un messager vint trouver Job et lui dit: « Les bœufs labouraient, et les ânes paissaient à côté d'eux,
15 sai Sabenawa suka auka musu suka kwashe su suka tafi, suka karkashe masu yi maka aiki duka, ni kaɗai na tsira na zo in gaya maka!”
mais les Sabéens ont attaqué et les ont emmenés. Oui, ils ont tué les serviteurs au fil de l'épée, et moi seul ai échappé pour te le dire. »
16 Yana cikin magana sai ga wani ɗan aika ya zo ya ce, “Wutar Allah ta sauko daga sama ta ƙona dukan tumaki da masu lura da su, wato, bayinka, ni kaɗai na tsira na zo in gaya maka!”
Comme il parlait encore, un autre vint aussi et dit: « Le feu de Dieu est tombé du ciel, il a brûlé les brebis et les serviteurs et les a consumés, et moi seul j'ai échappé pour vous le dire. »
17 Yana cikin magana sai ga wani ɗan aika ya zo ya ce, “Ƙungiyoyin mahara uku na Kaldiyawa sun auka wa raƙumanka sun kwashe su duka, suka kuma karkashe masu yi maka aiki, ni kaɗai ne na tsira na zo in gaya maka!”
Comme il parlait encore, un autre vint aussi et dit: « Les Chaldéens ont formé trois bandes et se sont jetés sur les chameaux, ils les ont emmenés, oui, et ils ont tué les serviteurs au fil de l'épée; moi seul, j'ai échappé pour vous le dire. »
18 Yana cikin magana, sai ga wani ɗan aika ya zo ya ce, “’Ya’yanka maza da mata suna biki, suna ci suna sha a gidan babban ɗanka,
Comme il parlait encore, un autre arriva, et dit: « Tes fils et tes filles mangeaient et buvaient du vin dans la maison de leur frère aîné,
19 sai wata iska mai ƙarfi daga hamada ta auka ta rushe gidan, gidan kuwa ya fāɗi a kan’ya’yanka ya kashe su, ni kaɗai na tsira na zo in gaya maka!”
et voici qu'un grand vent est venu du désert, il a frappé les quatre coins de la maison, il est tombé sur les jeunes gens, et ils sont morts. Moi seul, je me suis échappé pour vous le dire. »
20 Da jin haka sai Ayuba ya tashi ya yayyaga tufafin jikinsa, ya aske kansa. Ya fāɗi a ƙasa ya yi sujada
Alors Job se leva, déchira sa robe, se rasa la tête, se jeta à terre et se prosterna.
21 ya ce, “Tsirara na fito daga cikin mahaifiyata, tsirara kuma zan koma. Ubangiji ya bayar, Ubangiji kuma ya karɓa; yabo ya tabbata ga Ubangiji.”
Il dit: « Nu, je suis sorti du ventre de ma mère, et nu, j'y retournerai. Yahvé a donné, et Yahvé a repris. Que le nom de Yahvé soit béni. »
22 Cikin wannan duka Ayuba bai yi wa Allah zunubi ta wurin ba shi laifi ba.
Dans tout cela, Job n'a pas péché, ni accusé Dieu de mal faire.

< Ayuba 1 >